ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kyawawan Dabi’un Annabi Muhammadu (SAW)

by Dausayin Musulunci
2 years ago
Annabi

Masu karatu assalamu alaikum wa rahmtullahi ta’ala wa barkatuh. A darussanmu na baya, mun yi bayani kan abubuwan da aka hadu kan son yawaita su da wadanda ake kin yawaita su har muka dangana da zuhudu da tsarin adon Manzon Allah (SAW).

Yanzun kuma, za mu karkata zuwa kan kyawawan dabi’un Annabi Muhammadu (SAW).

Akwai dabi’u Wahabiyya: su ne wadanda Allah ya halicci mutum da su, ana cewa tun yana yaro haka halinsa yake. Akwai wadanda kuma mutum koya ya yi.

ADVERTISEMENT
  • Rayuwar Annabi Muhammadu (SAW) Da Abin Da Ya Ta’allaka Da Aurensa (1)
  • Darasi Na Biyu A Kan Matan Annabi (SAW)

Dabi’u wadanda ake tsururunsu, Malamai da masu hankali duk sun tafi cewa, dabi’u ne abin yabo ga mai ita ko da daya ce tak. Misali, wane mai hakuri ne ko mai kyauta ne da dai sauran su ballantana a ce ya tara daga cikin dabi’un da yawa ko da biyu ko uku ko fiye da haka. Dabi’u kyawawa 300 ne, Annabi (SAW) yana cewa, Allah Tabaraka wa ta’ala yana da dabi’u kyawawa guda 300 duk wanda ya siffantu da daya daga ciki zai shiga Aljannah.

Wadannan dabi’u, Shari’a ta yi yabo kuma ta yi alkawarin Aljannah ga ma’abocin daya daga cikinsu ballantana ka hada da yawa, su ne wadanda ake kira da kyawawan dabi’u “Husnul khuluki” dabi’u kyawawa suna daga cikin sashin Annabta, su ne daidaito cikin karfin zuciya da siffofinta, idan sadaukantaka Allah ya ba ka a zuciya sai a hada ta da hakuri – sadaukantaka babu hakuri zalunci kenan, in dukiya Allah ya wadata ka da ita, sai ya hada ta da kyauta, in shugabanci Allah ya ba ka sai ya hada ka da tausayi, in Malumta Allah ya ba ka, sai ya hadaka da soyayyar shiriyar mutane. Duk irin dabi’ar da Allah ya ba ka, sai ya hada ta da tsaka-tsaki.

LABARAI MASU NASABA

Hikimomin Kalaman Manzon Allah (SAW)

Maulidin Bana:Babu Wanda Ya Fi Cancanta Da Soyayya Saboda Gwarzontaka Kamar Annabi (SAW) —Mai Diwani

Shari’a ba ta son ka zama keke-da-keke, ma’ana kar ka yi sama kololuwa ba ka tsoron kowa kuma kar ka yi kasa can ka zama raggo, Shari’a tana son daidaito.

To mu sani cewa, duk wannan kyawawan dabi’un su ne dabi’un Annabinmu (SAW). Duk abubuwan da Allah ya bai wa Annabi (SAW) don mu san dabi’u su ne gaba, sai Allah ya yi kirari yana yabon Annabi (SAW) da cewa, Ya Rasulallahi, wallahi kana kan dabi’u masu girma da fadinsa cewa “Wa’innaka la’ala khulukin azim”. Sayyada A’isha tana cewa, dabi’un Annabi (SAW) su ne ‘Alkur’ani’ yana yarda da abin da alkur’ani ya yarda da shi, yana fushi da fushin Alkur’ani. “…kana khulukuhul kur’anu, yarda bi ridahu, wa yaskhadu bi sakhadihi”, Annabi (SAW) ya ce, Allah ya aiko ni don in cika kyawawan dabi’u “Bu’istu li’utimmima makarimal akhlaki” tun daga kan Annabi Adam (AS), akwai dabi’u kyawawa akwai na banza har aka zo kan Kuraishawa, don haka Annabi (SAW) ya ce, yanzun an aiko shi don cika kyawawan dabi’un kuma ya cika su, don haka yanzun, kowa sai ya yi koyi da na Annabi (SAW).

Anas Allah ya yarda dashi ya ce, Annabi (SAW) ya kasance mafificin mutane a kan kyawawan dabi’a, “kana Rasulallahi (SAW) ahsanan nasa khulukan” ba laifi ba ne a fi ka karatu da arziki amma kar ka bari a fi ka dabi’a.

An karvo daga Sayyadina Aliyu bin Abi Dalib, akan irin Hadisin da ya gabata daga Anas. Wani ya tambayi Sayyadina Ali a kan ya lissafa masa dabi’un Annabi (SAW), sai Sayyadina Ali ya ce masa kafin na fada maka, zan so ka fara lissafa min kayayyakin jin dadi da Allah ya ambata, sai ya ce suna da yawa ba za su lissafu ba, sai Sayyadina Ali ya ce, amma kuma Allah ya ce musu ‘yan kadan “Mata’ud duniya kalil…” ta yaya zan lissafa maka abin da Allah ya ce masa mai girma “Wa’innaka la’ala khulukin azim”.

Yana daga abin da Malamai muhakkikai (karshen yabon da za a yi wa Malami, a ce masa muhakkiki, wasu mutane ne daban suka vata wannan suna amma asalinta yana nan) suka tabbatar cewa, wadannan kyawawan dabi’u a kansu aka halicci Annabi (SAW). Mala’ikah Ridwan mai tsaron Aljannah, Allah ya dunkule ni’imarsa ce ya halicce shi da ita, Mala’ikah Maliku mai tsaron wuta, fushin Allah, Allah ya tattare ya haliice shi da ita. Don haka babu abin da zai zo ta wurin Ridwan sai ni’ima kamar yadda Malik babu komai sai fushi.

Annabi (SAW) babu abin da zai zo ta wurin shi sai Ni’imah, wani zai iya cewa ai ya yi yaki, yaki kuma azaba ce, sai mu ce masa wannan magani ne Annabi (SAW) ya ba da kamar irin yadda Uba yake bai wa Dansa magani madaci don yaron ya warke daga cuta ba don azabtarwa ba, kamar yadda Malamin makaranta ke dukan Dalibansa ba don azabtarwa ba sai don ladabtarwa.

Wanda ya samu tarihin Annabawa tun daga kuruciya har zuwa lokacin aiken Annabta, zai tabbatar da kyawawan dabi’un Annabawa, sabida ba koya suke yi ba, da ita ake halittarsu. Annabi (SAW) ya ce, Ubangijina ne ya ladabtar da ni kuma ya kyautata ladabtarwata “Addabani Rabbi fa ahsana ta’adibi” an ga irin wannan ladabtarwar a wurin Annabi Isah da Musa da Sulaiman da Yahya (Alaihimus salam) da sauransu.

Haka Allah ya halicce su da wadannan kyawawan dabi’un da Ilimin Hadarar Allah.

Amma wadanda ba su da wannan dole sai sun koya sun hadu da Malaman da suka sani, sannan su sanar da su kamar yadda aka sanar da su, in mai neman Allah ne ya samu Shehi ya ba shi azkaru tarbiyyati da dai dukkan fannin dabi’u.

Allah yana cewa cikin hakkin Annabi Yahya (AS) “wa atainahul hukma sabiyya” Malamai masu tafsiri suka ce, Allah ya bai wa Annabi Yahya Ilimin Injila, ya haddace, ya san lunguna da sako na ma’anoninta tun yana yaro. Malam Ma’amaru ya kara da cewa, tun yana dan shekara biyu ko uku ya san duk wadannan ma’anonin littafin. An ruwaito cewa, wata rana yara sun tambaye shi, wai me ya sa baka wasa? Sai ya ce musu, ba sabida wasa aka halicce ni ba.

Mahaifinsa Annabi Zakariya yana da kusan shekara 120, mahaifiyarsa tana da kusan shekara 80 Allah ya azurta su da samun Yaro (Annabi Yahya). A al’adar Mahaifi yana son wasa da dansa a lokacin kuruciya amma Annabi Yahya duk lokacin da a kai masa wasa, sai ya nuna rashin jin dadin wasan, har wata rana yake ce wa Mahaifinsa Annabi Zakariya (AS), wai kai wasa kazo yi Duniya ne? Hakan ta sa Annabi Zakariya ya koma kai kukansa ga Ubangiji kan halayen Dansa, Annabi Yahya. Sai Ubangiji ya ce masa, Ya Zakariya, kai ka roke ni in ba ka shi a haka a wurin addu’arka “Rabbi habli min ladunka waliyyya, yarisuni wa yarisu min ali ya’akub, waj’alhu rabbi radiyya” ka nema Ubangijinka ya ba ka Da waliyyi daga wurinsa kuma ya gaje ka da duk wani gadon gidan Annabi Ya’akub (Annabawa 124,000 duk ba ni Isra’ila ne sai ‘yan kadan) kuma Ubangiji ya sanya shi yardajje. Me irin wannan abubuwan ba zai iya tsayawa wasa ba.

An ruwaito cewa, Uba ya yi wasa da dansa a shekaru bakwai na haihuwa, ya karantar da shi a shekaru bakwai na biyu na haihuwa, ya zama abokin dansa a shekaru bakwai na Uku na haihuwa daga nan ya bar shi da makarantar Duniya.

Allah Ubangiji tabaraka wa ta’ala ya bayyana kalaman Annabi Isah (AS) ga mahaifiyarsa yayin haihuwa: “fa nadaha man tahtiha alla tahzani kad ja’ala rabbuki tahtaki sariyya” Sai wanda ke karkashinta, ya kirata da cewa, kar ki yi bakin ciki, lallai Ubangijinki ya sanya abin da ke kasanki ya zama farin ciki a gare ki.

Annabi
Dausayin Musulunci
+ postsBio
  • Dausayin Musulunci
    https://hausa.leadership.ng/author/dausayin-musulunci/
    Yadda Ake Fitar Da Zakkar Fidda Kai Da Sallar Idi
  • Dausayin Musulunci
    https://hausa.leadership.ng/author/dausayin-musulunci/
    Sadaukantaka, Kunya Da Kawar Da Kai Na Annabi Muhammadu (SAW)
  • Dausayin Musulunci
    https://hausa.leadership.ng/author/dausayin-musulunci/
    Hakuri Da Baiwa (Kyautar) Manzon Allah (SAW)
  • Dausayin Musulunci
    https://hausa.leadership.ng/author/dausayin-musulunci/
    Kyawawan Halaye 2: Wasu Annabawa Da Sauran Bayin Allah Da Suka Yi Magana A Tsumman Jego

MASU ALAKA

Hikimomin Kalaman Manzon Allah (SAW)
Dausayin Musulunci

Hikimomin Kalaman Manzon Allah (SAW)

September 4, 2026
Maulidin Bana:Babu Wanda Ya Fi Cancanta Da Soyayya Saboda Gwarzontaka Kamar Annabi (SAW) —Mai Diwani
Dausayin Musulunci

Maulidin Bana:Babu Wanda Ya Fi Cancanta Da Soyayya Saboda Gwarzontaka Kamar Annabi (SAW) —Mai Diwani

August 28, 2026
Annabi
Dausayin Musulunci

Hikimomin Kalaman Manzon Allah (SAW)

August 21, 2026
Next Post
Amfani Da Ganyen Doyar Da Aka Yi Wa Aure Na Kara Bunkasa Samar Da Ita- IITA

Amfani Da Ganyen Doyar Da Aka Yi Wa Aure Na Kara Bunkasa Samar Da Ita- IITA

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.