Tsohon Gwamnan Jihar Jigawa kuma jigo a jam’iyyar PDP, Sule Lamido, ya ce mutanen Arewacin Nijeriya su daina ganin laifin wani a waje, domin su kansu ne suka taka rawa wajen taɓarɓarewar tsaro a yankin.
Lamido ya bayyana hakan ne yayin wata hira da aka yi da shi a gidan rediyon Premier Radio da ke Kano a ranar Laraba.
Ya ce matsalar tsaro da ake fama da ita tana da alaƙa da rashin shugabanci na gari da kuma lalacewar tarbiyya a cikin al’umma.
A cewarsa, yawancin shugabannin siyasa sun yi watsi da aikinsu na kare rayuka da dukiyoyin jama’a, sun mayar da hankali kan siyasa maimakon shugabanci na gari.
Ya ce dole ne ‘yan Arewa su tashi tsaye su dawo da tarbiyya da ladabi ga matasa domin a magance matsalar tsaro.
Lamido ya kuma zargi wasu ‘yan siyasa da cewa suna amfani da matasa ta hanyar da ke lalata rayuwarsu, abin da ke ƙara ta’azzara matsalar rashin tsaro a yankin.
Ya ce waɗanda ke aikata laifuka kamar Boko Haram da fashi da makami ba baƙi ba ne, ‘yan yankin ne da suka taso a cikin al’umma.
A cewarsa, “’Ya’yanmu ne,” yana mai cewa matsalar ta samo asali ne daga lalacewar tarbiyya, wanda ya ce ita ya kamata a fara gyarawa tun daga gida.
Tsohon gwamnan ya kuma goyi bayan kafa ‘yansandan jihohi, amma ya ce dole ne a ba su horo mai kyau kafin fara aiki.
Ya ce abin takaici ne ganin yadda wasu daga cikin mutanen yankin ke sace juna ko aikata laifi ga ‘yan uwansu domin neman kuɗin fansa, yana mai cewa shugabanni sun fi mayar da hankali kan siyasa maimakon warware matsalolin jama’a.
A ƙarshe, Lamido ya ce adalci, gaskiya da tarbiyya su ne mafita wajen dawo da zaman lafiya a Arewacin Nijeriya.















Discussion about this post