ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Laifin ‘Yan Arewa Ne Kan Yadda Muka Bari Matsalar Tsaro Ta Addabe Mu — Sule Lamido

by Sadiq
2 weeks ago

Tsohon Gwamnan Jihar Jigawa kuma jigo a jam’iyyar PDP, Sule Lamido, ya ce mutanen Arewacin Nijeriya su daina ganin laifin wani a waje, domin su kansu ne suka taka rawa wajen taɓarɓarewar tsaro a yankin.

Lamido ya bayyana hakan ne yayin wata hira da aka yi da shi a gidan rediyon Premier Radio da ke Kano a ranar Laraba.

Ya ce matsalar tsaro da ake fama da ita tana da alaƙa da rashin shugabanci na gari da kuma lalacewar tarbiyya a cikin al’umma.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, yawancin shugabannin siyasa sun yi watsi da aikinsu na kare rayuka da dukiyoyin jama’a, sun mayar da hankali kan siyasa maimakon shugabanci na gari.

Ya ce dole ne ‘yan Arewa su tashi tsaye su dawo da tarbiyya da ladabi ga matasa domin a magance matsalar tsaro.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Lamido ya kuma zargi wasu ‘yan siyasa da cewa suna amfani da matasa ta hanyar da ke lalata rayuwarsu, abin da ke ƙara ta’azzara matsalar rashin tsaro a yankin.

Ya ce waɗanda ke aikata laifuka kamar Boko Haram da fashi da makami ba baƙi ba ne, ‘yan yankin ne da suka taso a cikin al’umma.

A cewarsa, “’Ya’yanmu ne,” yana mai cewa matsalar ta samo asali ne daga lalacewar tarbiyya, wanda ya ce ita ya kamata a fara gyarawa tun daga gida.

Tsohon gwamnan ya kuma goyi bayan kafa ‘yansandan jihohi, amma ya ce dole ne a ba su horo mai kyau kafin fara aiki.

Ya ce abin takaici ne ganin yadda wasu daga cikin mutanen yankin ke sace juna ko aikata laifi ga ‘yan uwansu domin neman kuɗin fansa, yana mai cewa shugabanni sun fi mayar da hankali kan siyasa maimakon warware matsalolin jama’a.

A ƙarshe, Lamido ya ce adalci, gaskiya da tarbiyya su ne mafita wajen dawo da zaman lafiya a Arewacin Nijeriya.

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Tinubu Ya Naɗa Mai Shekaru 39 A Matsayin Sabon Shugaban JAMB

Tinubu Ya Naɗa Mai Shekaru 39 A Matsayin Sabon Shugaban JAMB

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.