ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Laifin ‘Yan Arewa Ne Kan Yadda Muka Bari Matsalar Tsaro Ta Addabe Mu — Sule Lamido

by Sadiq
2 months ago

Tsohon Gwamnan Jihar Jigawa kuma jigo a jam’iyyar PDP, Sule Lamido, ya ce mutanen Arewacin Nijeriya su daina ganin laifin wani a waje, domin su kansu ne suka taka rawa wajen taɓarɓarewar tsaro a yankin.

Lamido ya bayyana hakan ne yayin wata hira da aka yi da shi a gidan rediyon Premier Radio da ke Kano a ranar Laraba.

Ya ce matsalar tsaro da ake fama da ita tana da alaƙa da rashin shugabanci na gari da kuma lalacewar tarbiyya a cikin al’umma.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, yawancin shugabannin siyasa sun yi watsi da aikinsu na kare rayuka da dukiyoyin jama’a, sun mayar da hankali kan siyasa maimakon shugabanci na gari.

Ya ce dole ne ‘yan Arewa su tashi tsaye su dawo da tarbiyya da ladabi ga matasa domin a magance matsalar tsaro.

LABARAI MASU NASABA

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Lamido ya kuma zargi wasu ‘yan siyasa da cewa suna amfani da matasa ta hanyar da ke lalata rayuwarsu, abin da ke ƙara ta’azzara matsalar rashin tsaro a yankin.

Ya ce waɗanda ke aikata laifuka kamar Boko Haram da fashi da makami ba baƙi ba ne, ‘yan yankin ne da suka taso a cikin al’umma.

A cewarsa, “’Ya’yanmu ne,” yana mai cewa matsalar ta samo asali ne daga lalacewar tarbiyya, wanda ya ce ita ya kamata a fara gyarawa tun daga gida.

Tsohon gwamnan ya kuma goyi bayan kafa ‘yansandan jihohi, amma ya ce dole ne a ba su horo mai kyau kafin fara aiki.

Ya ce abin takaici ne ganin yadda wasu daga cikin mutanen yankin ke sace juna ko aikata laifi ga ‘yan uwansu domin neman kuɗin fansa, yana mai cewa shugabanni sun fi mayar da hankali kan siyasa maimakon warware matsalolin jama’a.

A ƙarshe, Lamido ya ce adalci, gaskiya da tarbiyya su ne mafita wajen dawo da zaman lafiya a Arewacin Nijeriya.

MASU ALAKA

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi
Manyan Labarai

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

July 17, 2026
Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe
Manyan Labarai

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
Manyan Labarai

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Next Post
Tinubu Ya Naɗa Mai Shekaru 39 A Matsayin Sabon Shugaban JAMB

Tinubu Ya Naɗa Mai Shekaru 39 A Matsayin Sabon Shugaban JAMB

LABARAI MASU NASABA

Yawan Mu’amalar Kudi Tsakanin Mazauna Sin Da ’Yan Kasashen Waje Ya Hau Wani Sabon Matsayi A Tarihi

Yawan Mu’amalar Kudi Tsakanin Mazauna Sin Da ’Yan Kasashen Waje Ya Hau Wani Sabon Matsayi A Tarihi

July 17, 2026
Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

July 17, 2026
Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala

Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala

July 17, 2026
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Babban Taron AI Na Duniya Na 2026 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Babban Taron AI Na Duniya Na 2026 Tare Da Gabatar Da Jawabi

July 17, 2026
Falalar Salatut Tasbihi

Falalar Salatut Tasbihi

July 17, 2026
A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

July 17, 2026
Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

July 17, 2026
Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

July 17, 2026
Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026
Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.