ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Lauyoyin Bazoum Sun Bukaci Kotun ECOWAS Ta Mayar Da Shi Karagar Mulki

by Sadiq
3 years ago
Bazoum

Lauyoyin hambararen shugaban Jamhuriyar Nijar, Bazoum Mohammed sun bukaci kotun ECOWAS da ke zama a Nijeriya da ta mayar da shi kan karagar mulki, yayin da suka shaida mata cewar hambarar da shi da kuma tsare shi take hakkinsa ne na bil Adama.

Wannan ya biyo bayan juyin mulkin da sojoji suka yi wa zababben shugaban a ranar 26 ga watan Yuli tare da kuma tsare shi, saboda abin da suka kira gazawarsa ta samar da tsaro a fadin kasar da ke fuskantar matsalolin ‘yan ta’adda.

  • Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan N89.3
  • Gobara Ta Tashi A Shagon Sayar Da Kayan Kamfanin Samsung A Abuja

Lauyoyin shugaban sun gabatar da hujjojinsu da kuma bukatar amincewar kotun ta ECOWAS da ta mayar da Bazoum kan karagar mulki, duk da yake kasashe da dama basa mutunta umarninta.

ADVERTISEMENT

Daya daga cikin lauyoyin tsohon shugaban, Seydou Diagne ya shaida wa kotun cewar juyin mulkin da aka yi wa zababbiyar gwamnati take hakkin bil Adama ne.

Lauyan wanda ya yi wa kotun bayani ta bidiyo daga mazauninsa da ke Senegal, ya bukaci sakin Bazoum ba tare da gindaya sharidodi ba, yayin da ya kuma soki tsare uwargidansa da kuma dansa.

LABARAI MASU NASABA

Nijar Da Canada Sun Ƙulla Yarjejeniyar Gina Sabuwar Matatar Mai A Jihar Dosso

Kotun ICC Ta Yi Watsi Da Sabbin Takunkuman Amurka Kan Jami’anta

Lauyar da ke kare gwamnatin sojin Nijar, Aissatou Zada ta shaida wa kotun cewar ba a taka doka ba wajen tsare shugaba Bazoum, saboda an killace shi ne a gidansa domin kare lafiyarsa, kuma iyalansa na iya zuwa ganinsa lokacin da suke so.

Sai dai lauyoyin Bazoum sun ce tun daga ranar 20 ga watan Oktoba sun kasa magana da shi, bayan da sojoji suka yi zargin cewar yayi kokarin barin kasar.

Kotun ta sanya ranar 30 ga watan nan a matsayin ranar yanke hukunci a kan shari’ar.

MASU ALAKA

Bazoum
Kasashen Ketare

Nijar Da Canada Sun Ƙulla Yarjejeniyar Gina Sabuwar Matatar Mai A Jihar Dosso

August 23, 2026
Bazoum
Kasashen Ketare

Kotun ICC Ta Yi Watsi Da Sabbin Takunkuman Amurka Kan Jami’anta

August 23, 2026
Bazoum
Kasashen Ketare

Rasha Da Ukraine Sun Zafafa Hare-hare Kan Juna Bayan Yaƙinsu Ya Ɗauki Sabon Salo

August 22, 2026
Next Post
Za Mu Yi Wa ‘Yan TikTok Auren Gata – Hisba

Za Mu Yi Wa 'Yan TikTok Auren Gata - Hisba

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.