ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Lee Jae-Myung: Tabbas Za A Kyautata Hulda Tsakanin Koriya Ta Kudu Da Sin

by Sulaiman
5 months ago

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Kafin ya fara ziyara a kasar Sin a gobe Lahadi, shugaban kasar Koriya ta Kudu Lee Jae-myung, ya zanta da wata wakiliyar kafar CMG, inda ya bayyana imaninsa da huldar dake tsakanin kasarsa da kasar ta Sin, wadda ya ce za ta daga zuwa wani sabon matsayi, bisa tushen ziyarar da shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya kai Koriya ta Kudu a bara, gami da ziyarar da shi ma zai gudanar a kasar Sin a wannan karo.

Yayin da ya tabo batu kan ziyarar da ya gudanar a kasar Sin a lokutan baya, Lee Jae-myung ya ce, a duk lokacin da ya shiga kasar Sin, ya kan ji tamkar ya shiga wata sabuwar duniya, saboda manyan sauye-sauye da ci gaba da kasar Sin ke samu. A cewarsa, kasar Sin ta karkata ga raya bangaren makamashi masu sabuntawa cikin sauri, tare da samun babban sakamako, inda kasar ta zama kan gaba a duniya a wannan bangare, musamman ma a fannin hada na’urorin samar da lantarki ta hasken rana. Wannan batu, a cewar Lee, ya shaida kwarewar kasar Sin a fannin mayar da kalubale zuwa dama, da dora karfin kasa wajen kirkiro sabbin fasahohi, da jagorantar ci gaban masana’antu.

Sa’an nan, a lokacin da ya ambaci cudanyar da ya yi da takwaransa na kasar Sin Xi Jinping, Lee Jae-myung ya ce, shugaba Xi wani fitaccen shugaba ne mai hangen nesa, wanda za a iya hadin gwiwa, gami da kulla huldar taimakon juna da shi. A ganin Lee, ya kamata kasashen Sin da Koriya ta Kudu su yi kokarin neman bangarorin da za su iya rika hadin gwiwa da juna, don tabbatar da moriyar dukkan kasashen biyu, tare da kulla huldar amincewa da juna, da hadin kai, gami da cude-ni-in-cude-ka. Shugaba Lee ya kara da cewa, shugaba Xi Jinping ya fahimci wannan bukata sosai, kana shi da kansa yana da imani da cewa, za a iya mayar da bukatar ta zama sakamako na gaske.

ADVERTISEMENT

Ban da haka, Lee Jae-myung ya jaddada cewa, dangane da batun Taiwan, wanda kasar Sin ke dora matukar muhimmanci a kai, kasar Koriya ta Kudu za ta ci gaba da girmama manufar nan ta Sin daya tak a duniya, daidai da yadda kasar ke tsaye kan wannan matsayi a baya. (Bello Wang)

Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • Sulaiman
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

MASU ALAKA

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
Daga Birnin Sin

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Next Post
Sojoji Sun Kama Mai Tsara Harin Ƙunar Baƙin Wake A Arewa-Maso-Gabas

Sojoji Sun Kama Mai Tsara Harin Ƙunar Baƙin Wake A Arewa-Maso-Gabas

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.