ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Lokacin Da Duniya Ke Kira Ga Zaman Lafiya, Japan Ta Zabi “Sake Daukar Makamai”!

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 months ago
Japan

An bude taron share fage na dandalin tsaro na Xiangshan na shekara ta 2026 a birnin Beijing na kasar Sin jiya Juma’a. Wakilai sama da 120 daga kasashe fiye da 40, da kungiyoyin kasa da kasa sun hallarta tare da gudanar da tattaunawa kan jigon “Tsarin shugabancin tsaro na duniya: kalubale da mafita”. A wani bangare kuwa, Japan ta fara harba makamai masu kai hari ketare a karon farko, a atisayen hadin gwiwa na Amurka da Philippines na “kafada da kafada” a ranar 6 ga watan Mayu. Matakan sun nuna nau’ika biyu mabanbanta na yanayin tsaron duniya.

Duniya a yau ba ta cikin kwanciyar hankali. Yake-yake na ci gaba da dabaibayi Yankin Gabas ta Tsakiya, rikicin Ukraine ya dade yana wakana, kana wasu manyan kasashe suna daukar ra’ayin bangaranci, yayin da ikon Majalisar Dinkin Duniya ke fuskantar yiwuwar durkushewa. A daidai lokacin da dandalin tsaro na Xiangshan ke kokarin nazarin “mafitar zaman lafiya da tsaron duniya”, ’yan siyasa masu tsattsauran ra’ayi na Japan na kara hanzarta “sake daukar makamai don farfado da ra’ayin fin karfi”. A watan Afirilun bana sun sassauta dokar dake yi wa kasar tarnakin fitar da makamai masu kisa a hukumance. A ranar 6 ga watan Mayu kuma sun fara harba makamai masu kai hari a Philippines a karon farko a ketare. Kazalika, a ranar 8 ga watan Mayu, firaministan kasar Takaichi Sanae, ta bayyana a fili cewa shirinta na ziyartar Amurka yana da nufin “kara karfafa karfin takara”. A lokaci guda kuma, ‘yan majalisa 126 na Japan sun ziyarci haikalin Yasukuni, wato wurin tunawa da wadanda suka aikata lafin yaki. Kuma Japan tana ci gaba da hanzarta gyaran kundin tsarin mulkinta. Ba shakka daga fadada sojoji da gyaran kundin tsarin mulki zuwa ziyartar haikalin Yasukumi, Japan tana zama daya daga cikin manyan masu kawo rudani da rashin tabbaci a tsarin tsaron yankin Asiya da tekun Pasifik.

Sabanin manufar “tsaro ta ra’ayin bangaranci” na Japan, bana ake cika shekaru 20 da kafuwar dandalin tsaro na Xiangshan, wanda ya kasance yana bin manufar “tattaunawa cikin daidaito, da hadin gwiwa da koyi da juna”. A wannan taro, ana mayar da hankali kan batutuwa kamar “tsarin kasa da kasa da bin doka”, da “sabon kalubalen tsaro a yankin Asiya da tekun Pasifik”, kana da “Alhakin kiyaye tsaron duniya na hadin gwiwa” da sauransu.

ADVERTISEMENT

Shugabar ofishin dandalin Li Shuyin ta nuna cewa, dandalin ya mai da hankali kan tsarin shugabancin tsaro na duniya, domin inganta aiwatar da shawarar shugaban kasar Sin Xi Jinping ta kyautata shugabancin duniya, da kuma magance matsalar gibin zaman lafiya, da gibin tsaro da gibin shugabanci.

A gefe guda, Japan tana harba makamai a ketare, tare da keta kundin tsarin mulkin zaman lafiya na bayan yakin duniya na biyu.

LABARAI MASU NASABA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

A gefe guda kuma, wakilai sama da 120 daga kasashe daban-daban suna tattaunawa, da gudanar da shawarwari a birnin Beijing domin neman hanyoyin zaman lafiya.

Hanyoyi biyu, makoma biyu ne. Kamar yadda Li Shuyin ta fada, muna bukatar “Mu bar kowace kasa ta tattauna tare duba da yanayin da ake ciki, ta yadda za a inganta kiyaye tsarin kasa da kasa, da bin dokar kasa da kasa.

“Lokacin da ’yan majalisa masu tsattsauran ra’ayi na Japan ke yunkurin ta da zaune tsaye a Asiya kamar yadda kasar ta taba yi, dandalin ya fitar da sako cewa, ba za a iya inganta tsarin shugabancin duniya ba, har sai an yi tattaunawa bisa daidaito da hadin kai da koyi da juna. (Marubuciya: MINA)

Japan
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
Japan
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

MASU ALAKA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026
Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Next Post
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada

NDLEA Ta Kai Mamaya Jami’ar BUK Ta Cafke Mutum 6 Da Ake Zargi

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.