ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Lokacin Da Duniya Ke Kira Ga Zaman Lafiya, Japan Ta Zabi “Sake Daukar Makamai”!

by CGTN Hausa and Sulaiman
4 weeks ago
Japan

An bude taron share fage na dandalin tsaro na Xiangshan na shekara ta 2026 a birnin Beijing na kasar Sin jiya Juma’a. Wakilai sama da 120 daga kasashe fiye da 40, da kungiyoyin kasa da kasa sun hallarta tare da gudanar da tattaunawa kan jigon “Tsarin shugabancin tsaro na duniya: kalubale da mafita”. A wani bangare kuwa, Japan ta fara harba makamai masu kai hari ketare a karon farko, a atisayen hadin gwiwa na Amurka da Philippines na “kafada da kafada” a ranar 6 ga watan Mayu. Matakan sun nuna nau’ika biyu mabanbanta na yanayin tsaron duniya.

Duniya a yau ba ta cikin kwanciyar hankali. Yake-yake na ci gaba da dabaibayi Yankin Gabas ta Tsakiya, rikicin Ukraine ya dade yana wakana, kana wasu manyan kasashe suna daukar ra’ayin bangaranci, yayin da ikon Majalisar Dinkin Duniya ke fuskantar yiwuwar durkushewa. A daidai lokacin da dandalin tsaro na Xiangshan ke kokarin nazarin “mafitar zaman lafiya da tsaron duniya”, ’yan siyasa masu tsattsauran ra’ayi na Japan na kara hanzarta “sake daukar makamai don farfado da ra’ayin fin karfi”. A watan Afirilun bana sun sassauta dokar dake yi wa kasar tarnakin fitar da makamai masu kisa a hukumance. A ranar 6 ga watan Mayu kuma sun fara harba makamai masu kai hari a Philippines a karon farko a ketare. Kazalika, a ranar 8 ga watan Mayu, firaministan kasar Takaichi Sanae, ta bayyana a fili cewa shirinta na ziyartar Amurka yana da nufin “kara karfafa karfin takara”. A lokaci guda kuma, ‘yan majalisa 126 na Japan sun ziyarci haikalin Yasukuni, wato wurin tunawa da wadanda suka aikata lafin yaki. Kuma Japan tana ci gaba da hanzarta gyaran kundin tsarin mulkinta. Ba shakka daga fadada sojoji da gyaran kundin tsarin mulki zuwa ziyartar haikalin Yasukumi, Japan tana zama daya daga cikin manyan masu kawo rudani da rashin tabbaci a tsarin tsaron yankin Asiya da tekun Pasifik.

Sabanin manufar “tsaro ta ra’ayin bangaranci” na Japan, bana ake cika shekaru 20 da kafuwar dandalin tsaro na Xiangshan, wanda ya kasance yana bin manufar “tattaunawa cikin daidaito, da hadin gwiwa da koyi da juna”. A wannan taro, ana mayar da hankali kan batutuwa kamar “tsarin kasa da kasa da bin doka”, da “sabon kalubalen tsaro a yankin Asiya da tekun Pasifik”, kana da “Alhakin kiyaye tsaron duniya na hadin gwiwa” da sauransu.

ADVERTISEMENT

Shugabar ofishin dandalin Li Shuyin ta nuna cewa, dandalin ya mai da hankali kan tsarin shugabancin tsaro na duniya, domin inganta aiwatar da shawarar shugaban kasar Sin Xi Jinping ta kyautata shugabancin duniya, da kuma magance matsalar gibin zaman lafiya, da gibin tsaro da gibin shugabanci.

A gefe guda, Japan tana harba makamai a ketare, tare da keta kundin tsarin mulkin zaman lafiya na bayan yakin duniya na biyu.

LABARAI MASU NASABA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

A gefe guda kuma, wakilai sama da 120 daga kasashe daban-daban suna tattaunawa, da gudanar da shawarwari a birnin Beijing domin neman hanyoyin zaman lafiya.

Hanyoyi biyu, makoma biyu ne. Kamar yadda Li Shuyin ta fada, muna bukatar “Mu bar kowace kasa ta tattauna tare duba da yanayin da ake ciki, ta yadda za a inganta kiyaye tsarin kasa da kasa, da bin dokar kasa da kasa.

“Lokacin da ’yan majalisa masu tsattsauran ra’ayi na Japan ke yunkurin ta da zaune tsaye a Asiya kamar yadda kasar ta taba yi, dandalin ya fitar da sako cewa, ba za a iya inganta tsarin shugabancin duniya ba, har sai an yi tattaunawa bisa daidaito da hadin kai da koyi da juna. (Marubuciya: MINA)

Japan
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
Japan
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki
Ra'ayi Riga

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

June 3, 2026
Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka
Ra'ayi Riga

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

June 1, 2026
Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya

May 29, 2026
Next Post
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada

NDLEA Ta Kai Mamaya Jami’ar BUK Ta Cafke Mutum 6 Da Ake Zargi

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa Da Wasu Ma’aurata A Abuja

Ƴansanda Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa Da Wasu Ma’aurata A Abuja

June 5, 2026
Kotu Ta Yi Gwanjon Kaddarorin Sani Sha’aban Bisa Taurin Bashi

Kotu Ta Yi Gwanjon Kaddarorin Sani Sha’aban Bisa Taurin Bashi

June 5, 2026
An Yi Suka Kan Mayar Da Nijeriya Jujin Jibge Kwantaina Da Ake Shigowa Da Su

An Yi Suka Kan Mayar Da Nijeriya Jujin Jibge Kwantaina Da Ake Shigowa Da Su

June 5, 2026
Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho

Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho

June 5, 2026
Sabon Rikicin Manoma Da Makiyaya yayi Ajalin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Sabon Rikicin Manoma Da Makiyaya yayi Ajalin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 5, 2026
Babu Wani Shiri Na Kwaso ‘Yan Nijeriya Daga Falasdin Ko Isra’ila –Gwamnatin Tarayya

Mulkin Tinubu A Shekara 3:Ina Aka Fito? Ina Aka Dosa?

June 5, 2026
Hajji 2026: Mahajjata 1,905 Sun Dawo Nijeriya Daga Saudiyya

Hajji 2026: Mahajjata 1,905 Sun Dawo Nijeriya Daga Saudiyya

June 5, 2026
Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

June 5, 2026
Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.