An bude taron share fage na dandalin tsaro na Xiangshan na shekara ta 2026 a birnin Beijing na kasar Sin jiya Juma’a. Wakilai sama da 120 daga kasashe fiye da 40, da kungiyoyin kasa da kasa sun hallarta tare da gudanar da tattaunawa kan jigon “Tsarin shugabancin tsaro na duniya: kalubale da mafita”. A wani bangare kuwa, Japan ta fara harba makamai masu kai hari ketare a karon farko, a atisayen hadin gwiwa na Amurka da Philippines na “kafada da kafada” a ranar 6 ga watan Mayu. Matakan sun nuna nau’ika biyu mabanbanta na yanayin tsaron duniya.
Duniya a yau ba ta cikin kwanciyar hankali. Yake-yake na ci gaba da dabaibayi Yankin Gabas ta Tsakiya, rikicin Ukraine ya dade yana wakana, kana wasu manyan kasashe suna daukar ra’ayin bangaranci, yayin da ikon Majalisar Dinkin Duniya ke fuskantar yiwuwar durkushewa. A daidai lokacin da dandalin tsaro na Xiangshan ke kokarin nazarin “mafitar zaman lafiya da tsaron duniya”, ’yan siyasa masu tsattsauran ra’ayi na Japan na kara hanzarta “sake daukar makamai don farfado da ra’ayin fin karfi”. A watan Afirilun bana sun sassauta dokar dake yi wa kasar tarnakin fitar da makamai masu kisa a hukumance. A ranar 6 ga watan Mayu kuma sun fara harba makamai masu kai hari a Philippines a karon farko a ketare. Kazalika, a ranar 8 ga watan Mayu, firaministan kasar Takaichi Sanae, ta bayyana a fili cewa shirinta na ziyartar Amurka yana da nufin “kara karfafa karfin takara”. A lokaci guda kuma, ‘yan majalisa 126 na Japan sun ziyarci haikalin Yasukuni, wato wurin tunawa da wadanda suka aikata lafin yaki. Kuma Japan tana ci gaba da hanzarta gyaran kundin tsarin mulkinta. Ba shakka daga fadada sojoji da gyaran kundin tsarin mulki zuwa ziyartar haikalin Yasukumi, Japan tana zama daya daga cikin manyan masu kawo rudani da rashin tabbaci a tsarin tsaron yankin Asiya da tekun Pasifik.
Sabanin manufar “tsaro ta ra’ayin bangaranci” na Japan, bana ake cika shekaru 20 da kafuwar dandalin tsaro na Xiangshan, wanda ya kasance yana bin manufar “tattaunawa cikin daidaito, da hadin gwiwa da koyi da juna”. A wannan taro, ana mayar da hankali kan batutuwa kamar “tsarin kasa da kasa da bin doka”, da “sabon kalubalen tsaro a yankin Asiya da tekun Pasifik”, kana da “Alhakin kiyaye tsaron duniya na hadin gwiwa” da sauransu.
Shugabar ofishin dandalin Li Shuyin ta nuna cewa, dandalin ya mai da hankali kan tsarin shugabancin tsaro na duniya, domin inganta aiwatar da shawarar shugaban kasar Sin Xi Jinping ta kyautata shugabancin duniya, da kuma magance matsalar gibin zaman lafiya, da gibin tsaro da gibin shugabanci.
A gefe guda, Japan tana harba makamai a ketare, tare da keta kundin tsarin mulkin zaman lafiya na bayan yakin duniya na biyu.
A gefe guda kuma, wakilai sama da 120 daga kasashe daban-daban suna tattaunawa, da gudanar da shawarwari a birnin Beijing domin neman hanyoyin zaman lafiya.
Hanyoyi biyu, makoma biyu ne. Kamar yadda Li Shuyin ta fada, muna bukatar “Mu bar kowace kasa ta tattauna tare duba da yanayin da ake ciki, ta yadda za a inganta kiyaye tsarin kasa da kasa, da bin dokar kasa da kasa.
“Lokacin da ’yan majalisa masu tsattsauran ra’ayi na Japan ke yunkurin ta da zaune tsaye a Asiya kamar yadda kasar ta taba yi, dandalin ya fitar da sako cewa, ba za a iya inganta tsarin shugabancin duniya ba, har sai an yi tattaunawa bisa daidaito da hadin kai da koyi da juna. (Marubuciya: MINA)















Discussion about this post