ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Lokacin Da Duniya Ke Kira Ga Zaman Lafiya, Japan Ta Zabi “Sake Daukar Makamai”!

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 months ago
Japan

An bude taron share fage na dandalin tsaro na Xiangshan na shekara ta 2026 a birnin Beijing na kasar Sin jiya Juma’a. Wakilai sama da 120 daga kasashe fiye da 40, da kungiyoyin kasa da kasa sun hallarta tare da gudanar da tattaunawa kan jigon “Tsarin shugabancin tsaro na duniya: kalubale da mafita”. A wani bangare kuwa, Japan ta fara harba makamai masu kai hari ketare a karon farko, a atisayen hadin gwiwa na Amurka da Philippines na “kafada da kafada” a ranar 6 ga watan Mayu. Matakan sun nuna nau’ika biyu mabanbanta na yanayin tsaron duniya.

Duniya a yau ba ta cikin kwanciyar hankali. Yake-yake na ci gaba da dabaibayi Yankin Gabas ta Tsakiya, rikicin Ukraine ya dade yana wakana, kana wasu manyan kasashe suna daukar ra’ayin bangaranci, yayin da ikon Majalisar Dinkin Duniya ke fuskantar yiwuwar durkushewa. A daidai lokacin da dandalin tsaro na Xiangshan ke kokarin nazarin “mafitar zaman lafiya da tsaron duniya”, ’yan siyasa masu tsattsauran ra’ayi na Japan na kara hanzarta “sake daukar makamai don farfado da ra’ayin fin karfi”. A watan Afirilun bana sun sassauta dokar dake yi wa kasar tarnakin fitar da makamai masu kisa a hukumance. A ranar 6 ga watan Mayu kuma sun fara harba makamai masu kai hari a Philippines a karon farko a ketare. Kazalika, a ranar 8 ga watan Mayu, firaministan kasar Takaichi Sanae, ta bayyana a fili cewa shirinta na ziyartar Amurka yana da nufin “kara karfafa karfin takara”. A lokaci guda kuma, ‘yan majalisa 126 na Japan sun ziyarci haikalin Yasukuni, wato wurin tunawa da wadanda suka aikata lafin yaki. Kuma Japan tana ci gaba da hanzarta gyaran kundin tsarin mulkinta. Ba shakka daga fadada sojoji da gyaran kundin tsarin mulki zuwa ziyartar haikalin Yasukumi, Japan tana zama daya daga cikin manyan masu kawo rudani da rashin tabbaci a tsarin tsaron yankin Asiya da tekun Pasifik.

Sabanin manufar “tsaro ta ra’ayin bangaranci” na Japan, bana ake cika shekaru 20 da kafuwar dandalin tsaro na Xiangshan, wanda ya kasance yana bin manufar “tattaunawa cikin daidaito, da hadin gwiwa da koyi da juna”. A wannan taro, ana mayar da hankali kan batutuwa kamar “tsarin kasa da kasa da bin doka”, da “sabon kalubalen tsaro a yankin Asiya da tekun Pasifik”, kana da “Alhakin kiyaye tsaron duniya na hadin gwiwa” da sauransu.

ADVERTISEMENT

Shugabar ofishin dandalin Li Shuyin ta nuna cewa, dandalin ya mai da hankali kan tsarin shugabancin tsaro na duniya, domin inganta aiwatar da shawarar shugaban kasar Sin Xi Jinping ta kyautata shugabancin duniya, da kuma magance matsalar gibin zaman lafiya, da gibin tsaro da gibin shugabanci.

A gefe guda, Japan tana harba makamai a ketare, tare da keta kundin tsarin mulkin zaman lafiya na bayan yakin duniya na biyu.

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

A gefe guda kuma, wakilai sama da 120 daga kasashe daban-daban suna tattaunawa, da gudanar da shawarwari a birnin Beijing domin neman hanyoyin zaman lafiya.

Hanyoyi biyu, makoma biyu ne. Kamar yadda Li Shuyin ta fada, muna bukatar “Mu bar kowace kasa ta tattauna tare duba da yanayin da ake ciki, ta yadda za a inganta kiyaye tsarin kasa da kasa, da bin dokar kasa da kasa.

“Lokacin da ’yan majalisa masu tsattsauran ra’ayi na Japan ke yunkurin ta da zaune tsaye a Asiya kamar yadda kasar ta taba yi, dandalin ya fitar da sako cewa, ba za a iya inganta tsarin shugabancin duniya ba, har sai an yi tattaunawa bisa daidaito da hadin kai da koyi da juna. (Marubuciya: MINA)

Japan
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta
Japan
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara
  • Sulaiman
    Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta
  • Sulaiman
    Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita
  • Sulaiman
    Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

MASU ALAKA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya
Ra'ayi Riga

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

June 19, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”
Ra'ayi Riga

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Next Post
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada

NDLEA Ta Kai Mamaya Jami’ar BUK Ta Cafke Mutum 6 Da Ake Zargi

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

June 25, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

June 25, 2026
Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

June 25, 2026
Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

June 25, 2026
Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.