Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Kasa (NDLEA) ta kai samame yankin Jami’ar Bayero Kano (BUK), inda ta kama mutum shida da ake zargi da harkar miyagun kwayoyi.
A yayin aikin, an kuma rusa wasu wuraren da ake zargin ana amfani da su wajen sayarwa da shan miyagun kwayoyi a cikin yankin da kewaye.
Wannan samame ya biyo bayan damuwar da ake ta nunawa kan yadda ake amfani da yankunan da ke kusa da manyan makarantu wajen safarar miyagun kwayoyi da shaye-shaye, lamarin da hukumomi ke cewa na barazana ga dalibai, ma’aikata da al’ummomin da ke makotaka.
Kakakin hukumar NDLEA na Kano, Sadik Maigatari, ya tabbatar da samamen a wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin, inda ya ce an gudanar da aikin ne karkashin jagorancin Kwamanda CN DY Lawal.
Ya ce an gudanar da aikin ne a karkashin shirin “Operation Sharar Mafaka” bayan korafi daga hukumar jami’ar kan ayyukan dillalan miyagun kwayoyi a wasu sassan makarantar da kewayenta.
Maigatari ya bayyana cewa an kama mutum shida yayin samamen, sannan an kwace tare da lalata wasu abubuwan da ke da alaka da haramtattun ayyukan.
Ya ce wannan mataki na nuna kudirin hukumar na tabbatar da muhalli mara miyagun kwayoyi, inda dalibai da ma’aikata za su zauna lafiya.
Hukumar ta kuma yaba wa shugabancin jami’ar Bayero Kano bisa gaggawar bayar da rahoto da kuma hadin gwiwa da hukumomin tsaro.
NDLEA ta gargadi mutane da su guji amfani da wuraren gwamnati ko cibiyoyin ilimi wajen harkar miyagun kwayoyi, tana mai cewa ba za ta lamunci hakan ba.
Ta kuma bukaci jama’a da cibiyoyi su ci gaba da ba da bayanai kan duk wani abin zargi domin taimakawa wajen gano da rusa wuraren boye miyagun kwayoyi a fadin jihar.















Discussion about this post