• English
  • Business News
Wednesday, July 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisa Ta 10: Sanatoci 24 Da Suka Shekara Cur Ba Su Kawo Kudiri Ba

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Labarai, Siyasa
0
Majalisa Ta 10: Sanatoci 24 Da Suka Shekara Cur Ba Su Kawo Kudiri Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kusan shekara guda daya da kaddamar da majalisa ta 10, amma har yanzu akwi sanatoci 24 ciki 109 daga sassan kasar nan da ba su kawo ko da kudiri guda daya ba a zauren majalisar dattawa. Sauran sanatocin guda 85 sun gabatar da kuduri daya ko fiye da haka.

An dai kaddamar da zauren majalisar dattawan ne a ranar 13 ga Yunin 2023, yayin da a yanzu ta zarce shekara guda. Bincike ya nuna cewa a zuwa yanzu an gabatar da kudirori 279 a zauren majalisa a tsakanin ranar 13 Yulin 2023 zuwa Maris ta 2024.

Daya daga cikin muhimman ayyukan ‘yan majalisa shi ne, su gabatar da kudirin kan abubuwan da suke ci wa al’ummarsu tuwo a kwarya a zauren majalisa.

  • Nan Ba Da Jimawa Ba Majalisa Za Ta Karbi Ƙudurin Sabon Mafi Karancin Albashi – Tinubu
  • ‘Yan Majalisar Wakilai Sun BuÆ™aci A Mayar Da Wa’adin Mulkin Nijeriya Falle ÆŠaya Mai Shekaru 6

Majalisar dattijai tana da mambobi 109, wanda 14 daga cikinsu tsofaffin gwamnoni ne, sai biyu daga cikin sanata da suka hada da Dabid Umahi (APC, Ebonyi ta Kudu), da Ibrahim Geidam (APC, Yobe ta Gabas) ne Shugaban kasa, Bola Tinubu ya nada ministocin ayyuka, da harkokin ‘yansanda.

Adadin tsoffin gwamnoni a majalisar dattawa ya karu bayan zuwan tsohon gwamnan Jihar Filato, Sanata Simon Lalong (APC, Filato ta Kudu) wanda aka rantsar da shi a matsayin sanata a watan Disambar 2023, don maye gurbin Sanata Napoleon Bali (PDP, Filato ta Kudu) bayan hukuncin kotun daukaka kara.

Labarai Masu Nasaba

Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano

Idan za a iya tunawa an rantsar da Sanata Ani, Dachungyang da Mustapha cikin majalisar dattawan a makare bayan da ‘yan majalisar suka tafi hutu. Yayin da Ani ya maye gurbin Umahi, Dachungyang ya maye gurbin tsohon shugaban marasa rinjaye, Mwadkwon Simon Dabou, sannan Mustapha ya maye gurbin Ibrahim Geidam.

Tsoffin gwamnonin da yanzu haka suke majalisar dattawa ta 10 su ne guda 13 da suka hada da Orji Uzor Kalu (APC, Abiya ta Arewa); Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio (APC, Akwa Ibom ta Arewa maso Yamma); Seriake Dickson (PDP, Bayelsa ta Yamma), Adams Oshiomhole (APC, Edo ta Arewa), Ibrahim Dankwambo (PDP, Gombe ta Arewa), Danjuma Goje (APC, Gombe ta tsakiya), Adamu Aliero (PDP, Kebbi ta tsakiya), Sani Bello (APC, Neja ta Arewa), Gbenga Daniel (APC, Ogun ta Gabas), Aminu Tambuwal (PDP, Sakkwato ta Kudu), Aliyu Wammako (APC, Sakkwato ta Arewa), Simon Lalong (APC, Filato ta Kudu da Abdulaziz Yari (APC, Zamfara ta Yamma).

Daga cikin tsofaffin gwamnoni 13, tara ne suka gabatar da kudirin a cikin wa’adin da aka yi nazari akai, wanda suka hada da Orji Uzor Kalu, kudiri 5; Shugaban Majalisar Dattawa Godswill Akpabio, biyu; Sanata Gbenga Daniel, 4; Sanata Dankwambo, 3; Aminu Tambuwal, 1; Sani Bello, 3; Danjuma Goje, 2; Wammako, 5; da Adamu Aliero, 1.

Cikin tsoffin gwamnonin da har yanzu ba su gabatar da wani kudirin doka ba a tsawon wannan lokaci sun hada da Sanata Adams Oshiomhole da Henry Seriake Dickson da Simon Lalong da kuma Abdulaziz Yari.

Sanatoci 24 baya ga tsofaffin gwamnoni hudu da har yanzu ba su dauki nauyin kowani kudiri ba sun hada da Sanata Ahmad Lawan (APC, Yobe ta Arewa), Bictor Umeh (LP, Anambra ta tsakiya), Oluwole Fasuyi Cyril (APC, Ekiti ta Arewa), Titus Tartenger Zam ( APC, Benuwai ta Arewa maso Yamma), Peter Jiya (PDP, Neja ta Kudu), Adegbonmire Adeniyi Ayodele (APC, Ondo ta tsakiya), Oyewumi Kamorudeen Olalere (PDP, Osun ta Yamma), Anthony Ani (APC, Ebonyi ta Kudu), Imasuen Neda Bernards ( LP, Edo ta Kudu); Okechukwu Ezea (LP, Inugu ta Arewa), Chukwu Chizoba (LP, Inugu ta Gabas), Abdul Ningi (PDP, Bauchi ta tsakiya), Khabeeb Mustapha (PDP, Jigawa ta Kudu maso Yamma) da Kaila Samaila Dahuwa (PDP, Bauchi ta Arewa).

Sauran sun hada da Sanata Rufai Hanga (NNPP, Kano ta tsakiya), Abdulaziz Yar’Adua (APC, Katsina ta tsakiya), Mohammed Dandutse Muntari (APC, Katsina ta Kudu), Enyinnaya Abaribe (APGA, Abiya ta Kudu), Pam Dachungyang (ADP, Filato ta Arewa); Onyesoh Allwell Heacho, (PDP, Ribas ta gabas); Ibrahim Lamido (APC, Sakkwato ta gabas), Manu Haruna (PDP, Taraba ta tsakiya) da Musa Mustapha (APC, Yobe

ta gabbas).


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan kalaremajalisaNijeriyaRepssenator
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Na Da Hakkin Shigar Da Kara Gaban WTO Kan Sabbin Harajin EU Kan EVs Na Sin

Next Post

Sin Na Maraba Da Goyon Bayan Duk Wani Kokari Da Zai Taimaka Wajen Tabbatar Da Zaman Lafiya

Related

Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari
Labarai

Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

3 hours ago
VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano
Labarai

VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano

3 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

6 hours ago
Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China
Labarai

Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China

7 hours ago
Girman Kai Da Son Zuciya Ba Za Su Sa A Amince Ko Ba Da Hadin Kai Ba
Ra'ayi Riga

Girman Kai Da Son Zuciya Ba Za Su Sa A Amince Ko Ba Da Hadin Kai Ba

9 hours ago
Bayan Shekaru 6 A Hannun Boko Haram, Wasu Yara Biyu Sun Kuɓuta
Labarai

Bayan Shekaru 6 A Hannun Boko Haram, Wasu Yara Biyu Sun Kuɓuta

9 hours ago
Next Post
Sin Na Maraba Da Goyon Bayan Duk Wani Kokari Da Zai Taimaka Wajen Tabbatar Da Zaman Lafiya

Sin Na Maraba Da Goyon Bayan Duk Wani Kokari Da Zai Taimaka Wajen Tabbatar Da Zaman Lafiya

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9

Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9

July 15, 2025
Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

July 15, 2025
VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano

VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano

July 15, 2025
Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

July 15, 2025
An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

July 15, 2025
Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

July 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

July 15, 2025
Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 

Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 

July 15, 2025
Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China

Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China

July 15, 2025
Taron Matasan Sin Da Afrika Kan Tsaro Zai Kirkiro Wata Sabuwar Mahanga Ta Magance Matsalolin Tsaro

Taron Matasan Sin Da Afrika Kan Tsaro Zai Kirkiro Wata Sabuwar Mahanga Ta Magance Matsalolin Tsaro

July 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.