ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisa Ta 10: Sanatoci 24 Da Suka Shekara Cur Ba Su Kawo Kudiri Ba

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Majalisa

Kusan shekara guda daya da kaddamar da majalisa ta 10, amma har yanzu akwi sanatoci 24 ciki 109 daga sassan kasar nan da ba su kawo ko da kudiri guda daya ba a zauren majalisar dattawa. Sauran sanatocin guda 85 sun gabatar da kuduri daya ko fiye da haka.

An dai kaddamar da zauren majalisar dattawan ne a ranar 13 ga Yunin 2023, yayin da a yanzu ta zarce shekara guda. Bincike ya nuna cewa a zuwa yanzu an gabatar da kudirori 279 a zauren majalisa a tsakanin ranar 13 Yulin 2023 zuwa Maris ta 2024.

Daya daga cikin muhimman ayyukan ‘yan majalisa shi ne, su gabatar da kudirin kan abubuwan da suke ci wa al’ummarsu tuwo a kwarya a zauren majalisa.

ADVERTISEMENT
  • Nan Ba Da Jimawa Ba Majalisa Za Ta Karbi Ƙudurin Sabon Mafi Karancin Albashi – Tinubu
  • ‘Yan Majalisar Wakilai Sun Buƙaci A Mayar Da Wa’adin Mulkin Nijeriya Falle Ɗaya Mai Shekaru 6

Majalisar dattijai tana da mambobi 109, wanda 14 daga cikinsu tsofaffin gwamnoni ne, sai biyu daga cikin sanata da suka hada da Dabid Umahi (APC, Ebonyi ta Kudu), da Ibrahim Geidam (APC, Yobe ta Gabas) ne Shugaban kasa, Bola Tinubu ya nada ministocin ayyuka, da harkokin ‘yansanda.

Adadin tsoffin gwamnoni a majalisar dattawa ya karu bayan zuwan tsohon gwamnan Jihar Filato, Sanata Simon Lalong (APC, Filato ta Kudu) wanda aka rantsar da shi a matsayin sanata a watan Disambar 2023, don maye gurbin Sanata Napoleon Bali (PDP, Filato ta Kudu) bayan hukuncin kotun daukaka kara.

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Idan za a iya tunawa an rantsar da Sanata Ani, Dachungyang da Mustapha cikin majalisar dattawan a makare bayan da ‘yan majalisar suka tafi hutu. Yayin da Ani ya maye gurbin Umahi, Dachungyang ya maye gurbin tsohon shugaban marasa rinjaye, Mwadkwon Simon Dabou, sannan Mustapha ya maye gurbin Ibrahim Geidam.

Tsoffin gwamnonin da yanzu haka suke majalisar dattawa ta 10 su ne guda 13 da suka hada da Orji Uzor Kalu (APC, Abiya ta Arewa); Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio (APC, Akwa Ibom ta Arewa maso Yamma); Seriake Dickson (PDP, Bayelsa ta Yamma), Adams Oshiomhole (APC, Edo ta Arewa), Ibrahim Dankwambo (PDP, Gombe ta Arewa), Danjuma Goje (APC, Gombe ta tsakiya), Adamu Aliero (PDP, Kebbi ta tsakiya), Sani Bello (APC, Neja ta Arewa), Gbenga Daniel (APC, Ogun ta Gabas), Aminu Tambuwal (PDP, Sakkwato ta Kudu), Aliyu Wammako (APC, Sakkwato ta Arewa), Simon Lalong (APC, Filato ta Kudu da Abdulaziz Yari (APC, Zamfara ta Yamma).

Daga cikin tsofaffin gwamnoni 13, tara ne suka gabatar da kudirin a cikin wa’adin da aka yi nazari akai, wanda suka hada da Orji Uzor Kalu, kudiri 5; Shugaban Majalisar Dattawa Godswill Akpabio, biyu; Sanata Gbenga Daniel, 4; Sanata Dankwambo, 3; Aminu Tambuwal, 1; Sani Bello, 3; Danjuma Goje, 2; Wammako, 5; da Adamu Aliero, 1.

Cikin tsoffin gwamnonin da har yanzu ba su gabatar da wani kudirin doka ba a tsawon wannan lokaci sun hada da Sanata Adams Oshiomhole da Henry Seriake Dickson da Simon Lalong da kuma Abdulaziz Yari.

Sanatoci 24 baya ga tsofaffin gwamnoni hudu da har yanzu ba su dauki nauyin kowani kudiri ba sun hada da Sanata Ahmad Lawan (APC, Yobe ta Arewa), Bictor Umeh (LP, Anambra ta tsakiya), Oluwole Fasuyi Cyril (APC, Ekiti ta Arewa), Titus Tartenger Zam ( APC, Benuwai ta Arewa maso Yamma), Peter Jiya (PDP, Neja ta Kudu), Adegbonmire Adeniyi Ayodele (APC, Ondo ta tsakiya), Oyewumi Kamorudeen Olalere (PDP, Osun ta Yamma), Anthony Ani (APC, Ebonyi ta Kudu), Imasuen Neda Bernards ( LP, Edo ta Kudu); Okechukwu Ezea (LP, Inugu ta Arewa), Chukwu Chizoba (LP, Inugu ta Gabas), Abdul Ningi (PDP, Bauchi ta tsakiya), Khabeeb Mustapha (PDP, Jigawa ta Kudu maso Yamma) da Kaila Samaila Dahuwa (PDP, Bauchi ta Arewa).

Sauran sun hada da Sanata Rufai Hanga (NNPP, Kano ta tsakiya), Abdulaziz Yar’Adua (APC, Katsina ta tsakiya), Mohammed Dandutse Muntari (APC, Katsina ta Kudu), Enyinnaya Abaribe (APGA, Abiya ta Kudu), Pam Dachungyang (ADP, Filato ta Arewa); Onyesoh Allwell Heacho, (PDP, Ribas ta gabas); Ibrahim Lamido (APC, Sakkwato ta gabas), Manu Haruna (PDP, Taraba ta tsakiya) da Musa Mustapha (APC, Yobe

ta gabbas).

Majalisa
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
Next Post
Sin Na Maraba Da Goyon Bayan Duk Wani Kokari Da Zai Taimaka Wajen Tabbatar Da Zaman Lafiya

Sin Na Maraba Da Goyon Bayan Duk Wani Kokari Da Zai Taimaka Wajen Tabbatar Da Zaman Lafiya

LABARAI MASU NASABA

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.