ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisa Ta 10: Sanatoci 24 Da Suka Shekara Cur Ba Su Kawo Kudiri Ba

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Majalisa

Kusan shekara guda daya da kaddamar da majalisa ta 10, amma har yanzu akwi sanatoci 24 ciki 109 daga sassan kasar nan da ba su kawo ko da kudiri guda daya ba a zauren majalisar dattawa. Sauran sanatocin guda 85 sun gabatar da kuduri daya ko fiye da haka.

An dai kaddamar da zauren majalisar dattawan ne a ranar 13 ga Yunin 2023, yayin da a yanzu ta zarce shekara guda. Bincike ya nuna cewa a zuwa yanzu an gabatar da kudirori 279 a zauren majalisa a tsakanin ranar 13 Yulin 2023 zuwa Maris ta 2024.

Daya daga cikin muhimman ayyukan ‘yan majalisa shi ne, su gabatar da kudirin kan abubuwan da suke ci wa al’ummarsu tuwo a kwarya a zauren majalisa.

ADVERTISEMENT
  • Nan Ba Da Jimawa Ba Majalisa Za Ta Karbi Ƙudurin Sabon Mafi Karancin Albashi – Tinubu
  • ‘Yan Majalisar Wakilai Sun Buƙaci A Mayar Da Wa’adin Mulkin Nijeriya Falle Ɗaya Mai Shekaru 6

Majalisar dattijai tana da mambobi 109, wanda 14 daga cikinsu tsofaffin gwamnoni ne, sai biyu daga cikin sanata da suka hada da Dabid Umahi (APC, Ebonyi ta Kudu), da Ibrahim Geidam (APC, Yobe ta Gabas) ne Shugaban kasa, Bola Tinubu ya nada ministocin ayyuka, da harkokin ‘yansanda.

Adadin tsoffin gwamnoni a majalisar dattawa ya karu bayan zuwan tsohon gwamnan Jihar Filato, Sanata Simon Lalong (APC, Filato ta Kudu) wanda aka rantsar da shi a matsayin sanata a watan Disambar 2023, don maye gurbin Sanata Napoleon Bali (PDP, Filato ta Kudu) bayan hukuncin kotun daukaka kara.

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

Idan za a iya tunawa an rantsar da Sanata Ani, Dachungyang da Mustapha cikin majalisar dattawan a makare bayan da ‘yan majalisar suka tafi hutu. Yayin da Ani ya maye gurbin Umahi, Dachungyang ya maye gurbin tsohon shugaban marasa rinjaye, Mwadkwon Simon Dabou, sannan Mustapha ya maye gurbin Ibrahim Geidam.

Tsoffin gwamnonin da yanzu haka suke majalisar dattawa ta 10 su ne guda 13 da suka hada da Orji Uzor Kalu (APC, Abiya ta Arewa); Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio (APC, Akwa Ibom ta Arewa maso Yamma); Seriake Dickson (PDP, Bayelsa ta Yamma), Adams Oshiomhole (APC, Edo ta Arewa), Ibrahim Dankwambo (PDP, Gombe ta Arewa), Danjuma Goje (APC, Gombe ta tsakiya), Adamu Aliero (PDP, Kebbi ta tsakiya), Sani Bello (APC, Neja ta Arewa), Gbenga Daniel (APC, Ogun ta Gabas), Aminu Tambuwal (PDP, Sakkwato ta Kudu), Aliyu Wammako (APC, Sakkwato ta Arewa), Simon Lalong (APC, Filato ta Kudu da Abdulaziz Yari (APC, Zamfara ta Yamma).

Daga cikin tsofaffin gwamnoni 13, tara ne suka gabatar da kudirin a cikin wa’adin da aka yi nazari akai, wanda suka hada da Orji Uzor Kalu, kudiri 5; Shugaban Majalisar Dattawa Godswill Akpabio, biyu; Sanata Gbenga Daniel, 4; Sanata Dankwambo, 3; Aminu Tambuwal, 1; Sani Bello, 3; Danjuma Goje, 2; Wammako, 5; da Adamu Aliero, 1.

Cikin tsoffin gwamnonin da har yanzu ba su gabatar da wani kudirin doka ba a tsawon wannan lokaci sun hada da Sanata Adams Oshiomhole da Henry Seriake Dickson da Simon Lalong da kuma Abdulaziz Yari.

Sanatoci 24 baya ga tsofaffin gwamnoni hudu da har yanzu ba su dauki nauyin kowani kudiri ba sun hada da Sanata Ahmad Lawan (APC, Yobe ta Arewa), Bictor Umeh (LP, Anambra ta tsakiya), Oluwole Fasuyi Cyril (APC, Ekiti ta Arewa), Titus Tartenger Zam ( APC, Benuwai ta Arewa maso Yamma), Peter Jiya (PDP, Neja ta Kudu), Adegbonmire Adeniyi Ayodele (APC, Ondo ta tsakiya), Oyewumi Kamorudeen Olalere (PDP, Osun ta Yamma), Anthony Ani (APC, Ebonyi ta Kudu), Imasuen Neda Bernards ( LP, Edo ta Kudu); Okechukwu Ezea (LP, Inugu ta Arewa), Chukwu Chizoba (LP, Inugu ta Gabas), Abdul Ningi (PDP, Bauchi ta tsakiya), Khabeeb Mustapha (PDP, Jigawa ta Kudu maso Yamma) da Kaila Samaila Dahuwa (PDP, Bauchi ta Arewa).

Sauran sun hada da Sanata Rufai Hanga (NNPP, Kano ta tsakiya), Abdulaziz Yar’Adua (APC, Katsina ta tsakiya), Mohammed Dandutse Muntari (APC, Katsina ta Kudu), Enyinnaya Abaribe (APGA, Abiya ta Kudu), Pam Dachungyang (ADP, Filato ta Arewa); Onyesoh Allwell Heacho, (PDP, Ribas ta gabas); Ibrahim Lamido (APC, Sakkwato ta gabas), Manu Haruna (PDP, Taraba ta tsakiya) da Musa Mustapha (APC, Yobe

ta gabbas).

Majalisa
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Labarai

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi
Labarai

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
Next Post
Sin Na Maraba Da Goyon Bayan Duk Wani Kokari Da Zai Taimaka Wajen Tabbatar Da Zaman Lafiya

Sin Na Maraba Da Goyon Bayan Duk Wani Kokari Da Zai Taimaka Wajen Tabbatar Da Zaman Lafiya

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.