ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisa Ta 10: Sanatoci 24 Da Suka Shekara Cur Ba Su Kawo Kudiri Ba

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Majalisa

Kusan shekara guda daya da kaddamar da majalisa ta 10, amma har yanzu akwi sanatoci 24 ciki 109 daga sassan kasar nan da ba su kawo ko da kudiri guda daya ba a zauren majalisar dattawa. Sauran sanatocin guda 85 sun gabatar da kuduri daya ko fiye da haka.

An dai kaddamar da zauren majalisar dattawan ne a ranar 13 ga Yunin 2023, yayin da a yanzu ta zarce shekara guda. Bincike ya nuna cewa a zuwa yanzu an gabatar da kudirori 279 a zauren majalisa a tsakanin ranar 13 Yulin 2023 zuwa Maris ta 2024.

Daya daga cikin muhimman ayyukan ‘yan majalisa shi ne, su gabatar da kudirin kan abubuwan da suke ci wa al’ummarsu tuwo a kwarya a zauren majalisa.

ADVERTISEMENT
  • Nan Ba Da Jimawa Ba Majalisa Za Ta Karbi Ƙudurin Sabon Mafi Karancin Albashi – Tinubu
  • ‘Yan Majalisar Wakilai Sun Buƙaci A Mayar Da Wa’adin Mulkin Nijeriya Falle Ɗaya Mai Shekaru 6

Majalisar dattijai tana da mambobi 109, wanda 14 daga cikinsu tsofaffin gwamnoni ne, sai biyu daga cikin sanata da suka hada da Dabid Umahi (APC, Ebonyi ta Kudu), da Ibrahim Geidam (APC, Yobe ta Gabas) ne Shugaban kasa, Bola Tinubu ya nada ministocin ayyuka, da harkokin ‘yansanda.

Adadin tsoffin gwamnoni a majalisar dattawa ya karu bayan zuwan tsohon gwamnan Jihar Filato, Sanata Simon Lalong (APC, Filato ta Kudu) wanda aka rantsar da shi a matsayin sanata a watan Disambar 2023, don maye gurbin Sanata Napoleon Bali (PDP, Filato ta Kudu) bayan hukuncin kotun daukaka kara.

LABARAI MASU NASABA

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

Idan za a iya tunawa an rantsar da Sanata Ani, Dachungyang da Mustapha cikin majalisar dattawan a makare bayan da ‘yan majalisar suka tafi hutu. Yayin da Ani ya maye gurbin Umahi, Dachungyang ya maye gurbin tsohon shugaban marasa rinjaye, Mwadkwon Simon Dabou, sannan Mustapha ya maye gurbin Ibrahim Geidam.

Tsoffin gwamnonin da yanzu haka suke majalisar dattawa ta 10 su ne guda 13 da suka hada da Orji Uzor Kalu (APC, Abiya ta Arewa); Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio (APC, Akwa Ibom ta Arewa maso Yamma); Seriake Dickson (PDP, Bayelsa ta Yamma), Adams Oshiomhole (APC, Edo ta Arewa), Ibrahim Dankwambo (PDP, Gombe ta Arewa), Danjuma Goje (APC, Gombe ta tsakiya), Adamu Aliero (PDP, Kebbi ta tsakiya), Sani Bello (APC, Neja ta Arewa), Gbenga Daniel (APC, Ogun ta Gabas), Aminu Tambuwal (PDP, Sakkwato ta Kudu), Aliyu Wammako (APC, Sakkwato ta Arewa), Simon Lalong (APC, Filato ta Kudu da Abdulaziz Yari (APC, Zamfara ta Yamma).

Daga cikin tsofaffin gwamnoni 13, tara ne suka gabatar da kudirin a cikin wa’adin da aka yi nazari akai, wanda suka hada da Orji Uzor Kalu, kudiri 5; Shugaban Majalisar Dattawa Godswill Akpabio, biyu; Sanata Gbenga Daniel, 4; Sanata Dankwambo, 3; Aminu Tambuwal, 1; Sani Bello, 3; Danjuma Goje, 2; Wammako, 5; da Adamu Aliero, 1.

Cikin tsoffin gwamnonin da har yanzu ba su gabatar da wani kudirin doka ba a tsawon wannan lokaci sun hada da Sanata Adams Oshiomhole da Henry Seriake Dickson da Simon Lalong da kuma Abdulaziz Yari.

Sanatoci 24 baya ga tsofaffin gwamnoni hudu da har yanzu ba su dauki nauyin kowani kudiri ba sun hada da Sanata Ahmad Lawan (APC, Yobe ta Arewa), Bictor Umeh (LP, Anambra ta tsakiya), Oluwole Fasuyi Cyril (APC, Ekiti ta Arewa), Titus Tartenger Zam ( APC, Benuwai ta Arewa maso Yamma), Peter Jiya (PDP, Neja ta Kudu), Adegbonmire Adeniyi Ayodele (APC, Ondo ta tsakiya), Oyewumi Kamorudeen Olalere (PDP, Osun ta Yamma), Anthony Ani (APC, Ebonyi ta Kudu), Imasuen Neda Bernards ( LP, Edo ta Kudu); Okechukwu Ezea (LP, Inugu ta Arewa), Chukwu Chizoba (LP, Inugu ta Gabas), Abdul Ningi (PDP, Bauchi ta tsakiya), Khabeeb Mustapha (PDP, Jigawa ta Kudu maso Yamma) da Kaila Samaila Dahuwa (PDP, Bauchi ta Arewa).

Sauran sun hada da Sanata Rufai Hanga (NNPP, Kano ta tsakiya), Abdulaziz Yar’Adua (APC, Katsina ta tsakiya), Mohammed Dandutse Muntari (APC, Katsina ta Kudu), Enyinnaya Abaribe (APGA, Abiya ta Kudu), Pam Dachungyang (ADP, Filato ta Arewa); Onyesoh Allwell Heacho, (PDP, Ribas ta gabas); Ibrahim Lamido (APC, Sakkwato ta gabas), Manu Haruna (PDP, Taraba ta tsakiya) da Musa Mustapha (APC, Yobe

ta gabbas).

Majalisa
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato
Manyan Labarai

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu
Rahotonni

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara
Labarai

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Next Post
Sin Na Maraba Da Goyon Bayan Duk Wani Kokari Da Zai Taimaka Wajen Tabbatar Da Zaman Lafiya

Sin Na Maraba Da Goyon Bayan Duk Wani Kokari Da Zai Taimaka Wajen Tabbatar Da Zaman Lafiya

LABARAI MASU NASABA

Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.