ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Majalisar Wakilai Sun Buƙaci A Mayar Da Wa’adin Mulkin Nijeriya Falle Ɗaya Mai Shekaru 6

by Naziru Adam Ibrahim
2 years ago
'Yan

Wata Ƙungiya ‘yan Majalisar wakilan Nijeriya su 30 da aka fi sani da “Reform Minded Lawmakers” daga Jam’iyyun Siyasa daban-daban (G-30), sun bayar da shawarar mayar da wa’adin mulke ɗaya ga Shugaban kasa na shekara shida da sauran Kujerun Mulki na shiya 6 na faɗin Nijeriya, cikin jerin kudurori da suka gabatar a gaban majalisar.

‘Yan majalisar sun kuma bayar da shawarar yadda za a gudanar da zaben shugaban ƙasa da na majalisar tarayya da na gwamnoni da na majalisun jihohi da na kananan hukumomi har da birnin tarayya duk a rana daya.

  • Majalisar Wakilai Za Ta Binciki CBN Kan Korar Ma’aikata 600
  • Yadda Wani Dan Majalisar Wakilan Nijeriya Ya Sha Da Kyar A Mazabarsa

‘Yan majalisar na “Reform Minded” sun bayyana hakan ne a lokacin da suke ganawa da manema labarai kan kudirori 50 da suka ɗauka, wadanda suka samu karatu na farko a zauren majalisar wakilan tarayya a Abuja ranar Litinin.

ADVERTISEMENT

Da yake karanta jawabin a taron manema labarai, ɗaya daga cikin yan Majalisun kuma mamba mai wakiltar mazabar Ideato ta Arewa da Kudanci Jihar Imo, Ikenga Imo Ugochinyere, ya ce suna bayar da shawarar yin gyare-gyare a kundin tsarin mulkin Nijeriya na 1999, don samar da tsarin karba-karba na zartaswa a tsakanin shiyyoyi shida na siyasa da ke ƙasarnan da zummar tabbatar da daidaiton wakilci tare da rage matsananciyar damuwa da tashin hankali da ma ƙirƙiro sabbin jihohi a Nijeriya.

Ugochinyere ya kuma nemi a gyara kundin tsarin mulkin ƙasa domin samar da ofishin mataimakan shugaban kasa biyu daga yankin kudu da arewacin Nijeriya, inda mataimakin na daya zai kasance mataimakin shugaban kasa, shi kuma mataimakin na biyu zai kasance minista mai kula da tattalin arziki.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

Ya ci gaba da cewa, ƙudirorin suna neman a yi wa kundin tsarin mulki gyara don ganin shugaban ƙasa da mataimakinsa na daya za su fito daga yanki daya na kasar nan (Arewa ko Kudu), kuma mataimakin shugaban ƙasa na daya zai zama shugaban ƙasa a duk lokacin da shugaban ƙasar ya gaza.

'Yan
Naziru Adam Ibrahim
+ postsBio
  • Naziru Adam Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/naziru-adam-ibrahim/
    Ya Kamata Farashin Siminti Ya Sauka — Umahi Ga Masana’antun Siminti
  • Naziru Adam Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/naziru-adam-ibrahim/
    Yari Ya Dace Da Rayuwar Mulki Da Kasuwanci
  • Naziru Adam Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/naziru-adam-ibrahim/
    A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara
  • Naziru Adam Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/naziru-adam-ibrahim/
    Shugaba Tinubu Ya Isa Nairobi Domin Halartar Taron Tattalin Arzikin Nahiyar Afirka

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Next Post
Masana’antun Samar Da Kayayyakin Masarufi Na Gudana Cikin Wani Yanayi Mai Armashi A Kasar Sin

Masana'antun Samar Da Kayayyakin Masarufi Na Gudana Cikin Wani Yanayi Mai Armashi A Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.