Mutane takwas sun rasu, yayin da gidaje da kadarorin miliyoyin kuɗi suka lalace sakamakon wata guguwa mai ƙarfi da ta afku a wasu yankuna da ke ƙaramar hukumar Bichi a Jihar Kano.
Bayan faruwar iftila’i, Majalisar Dokokin Jihar Kano, ta buƙaci gwamnatin jihar da ta gaggauta kai kayan agaji da tallafin jin-ƙai ga mutanen da abin ya shafa.
Majalisar ta cimma wannan matsaya ne bayan amincewa da ƙudirin gaggawa da ɗan majalisar mai wakiltar mazaɓar Bichi, Lawan Shehu, ya gabatar a zaman majalisar da Kakakin Majalisar, Jibril Falgore, ya jagoranta.
Shehu ya ce guguwar, wadda ta afku a ranar Alhamis da ta gabata, ta yi sanadin mutuwar mutane takwas tare da lalata gidaje da dama da sauran kadarori.
Ya ƙara da cewa ya kai ziyara yankunan da abin ya shafa tare da Shugaban Ƙaramar Hukumar Bichi domin jajanta wa iyalan mamatan da kuma duba irin ɓarnar da aka yi.
A cewarsa, ɗan majalisar mai wakiltar Bichi a Majalisar Wakilai ya bai wa kowane iyalin mamaci tallafin Naira miliyan biyu, yayin da iyalan da suka rasa ‘yan uwa da kuma kadarori suka samu tallafin Naira miliyan 10.
Daga bisani, ‘yan majalisar sun amince da ƙudirin tare da yin kira ga gwamnatin Gwamna Abba Kabir Yusuf da ta gaggauta kai kayan agaji da sauran tallafi ga mutanen da abin ya shafa.














