Malaman firamare da sakandare a Babban Birnin Tarayya (FCT) sun fara yajin aiki ba tare sai baba ta gani, lamarin da ya janyo rufe makarantu a Abuja. A safiyar Litinin, an gano makarantu kamar LEA Ijayapi da LEA Byazhin a karkashin AMAC a rufe, ba tare da malamai ko ɗalibai ba, yayin da ajujuwa suka kasance a kulle.
Matakin ya biyo bayan umarnin da Majalisar Zartarwa ta Ƙungiyar Malaman Nijeriya (NUT) reshen FCT ta bayar bayan wani taron gaggawa da aka yi a Gwagwalada ranar Juma’a. A cikin sanarwar da shugabannin ƙungiyar suka sanya wa hannu, an umurci malamai da su bi umarnin yajin aiki tare da jiran sabbin umarni.
- Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
- ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
- Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
- Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
- Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Ƙungiyar ta kuma shawarci iyaye su ajiye ‘ya’yansu a gida har sai an samu sabuwar sanarwa, tana mai cewa malamai ba za su koma bakin aiki ba har sai an biya musu bukatunsu. Ta bayyana cewa matakin ya biyo bayan karewar wa’adin kwanaki bakwai da aka bai wa Ministan FCT, Nyesom Wike, kan batutuwan walwala da daɗin malamai.
Duk da yaba wa ministan kan aiwatar da mafi ƙarancin albashi na N70,000 da biyan bashin albashi na watanni tara, ƙungiyar ta ce har yanzu akwai muhimman batutuwa da ba a warware ba. Daga cikin bukatunta akwai fitar da rahoton wani kwamiti da aka kafa, da cire sharadin “guraben aiki” da wajen karin girma, da kuma sake duba tsarin karin girma na shekarar 2024, tana mai jaddada cewa yajin aikin zai ci gaba har sai an magance wadannan matsaloli.














