Magoya bayan tsohon gwamnan Anambra, Peter Obi, da tsohon gwamnan Kano, Rabiu Kwankwaso, sun ƙaddamar da wata sabuwar ƙungiyar matsin lamba mai suna Obi–Kwankwaso (OK) Movement, yayin da ake ci gaba da sauye-sauyen siyasa gabanin zaɓen fidda gwani na jam’iyyar ADC a 2027.
Ƙungiyar ta bayyana hakan ne a Abuja, inda ta ce ta riga ta kafa tsare-tsare a dukkan jihohi 36 da Babban Birnin Tarayya tare da naɗa masu kula da yankuna.
Sakataren yaɗa labarai na ƙungiyar, Justin Ijeh, ya ce wannan haɗaka ce ta ƙungiyoyin siyasa daban-daban da suka haɗa da Obidient Movement, da Kwankwasiyya Movement, da NNPP da kuma ADC. Ya ce matakin na nuna sabon salo na haɗin gwuiwa a cikin ‘yan adawa yayin da ake fuskantar rashin tabbas kan wanda zai lashe tikitin takarar shugaban ƙasa na ADC.
- Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
- Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027
- Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
- ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
- Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Ijeh ya bayyana cewa ƙungiyar na neman haɗa kan ‘yan Nijeriya domin fuskantar ƙalubalen tattalin arziƙi da rashin tsaro, yana mai cewa za su fara ƙaddamar da rassan jihohi nan ba da jimawa ba. A nasa ɓangaren, jagoran Obidient Movement, Dr. Yunusa Tanko, ya tabbatar da cewa babu saɓani tsakanin wannan ƙungiyar da sauran ƙungiyoyin masu goyon bayan Obi, yana mai cewa duk suna aiki ne domin cimma buri guda.
Fitowar ƙungiyar ta OK Movement na zuwa ne yayin da ake samun rikici a cikin ADC kan burin tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, wanda ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takara ba tare da janyewa ba.
Haka kuma, wasu manyan ‘yan siyasa kamar Rotimi Amaechi, da Aminu Tambuwal da Nasir El-Rufai na cikin waɗanda ake hasashen za su nemi tikitin jam’iyyar, yayin da jam’iyyar Labour Party ta musanta wasu saƙonnin da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke kira ga Obi da Kwankwaso su koma cikinta.














