ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 6, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Maraba Da Ayyana Dokar Ta Ɓaci Kan Matsalar Tsaro A Nijeriya

by Ra'ayinmu
7 months ago
Maraba

Bisa wasu rahoatnin da kafafen yaɗa labarai suka wallafa, wasu ƴan ƙasar, sun yi hasashen cewa, ƙasar ba wai kawai na ci gaba da fuskantar matsalar tsaro ba ne.

Misali, mayaƙan ƙungiyar ƴan ta’adda ta ISWAP, a kwanan baya ta yiwa tawagar wasu dakarun soji kwanton Ɓauna a  babbar hanyar Damboa, da ke a jihar Borno, inda suka kama Birgediya Janar M. Uba, da ransa, suka kuma yi masa kisan gilla.

  • Shugaba Tinubu Ya Rantsar Da Janar Musa A Matsayin Ministan Tsaro
  • Sin Da Rasha Sun Yi Shawarwari Kan Manyan Tsare-tsaren Tsaro

Hakan ya nuna cewa, waɗannan ƴan ta’addar ba wai kawai masu akita muggan laifuka na je ken a yi bane, musamman duba da cewa, su kan kasance, ɗauke da muggan makamai, a duk lokacin da za su kai hare-harensu.

ADVERTISEMENT

Kazalika, a kwanan bayan gungun wasu ƴan bindiga sama da 30, ɗauke da muggan makamai a kan Babura, sun aukawa ƙauyen Fegin Baza na jihar Zamfara, suka hallaka mutane uku cikinsu har da wani jigo na jam’iyyar APC, tare da kuma sace wasu fararen Hula 64 da mata da kuma yara.

Wasu rahotannin sun ce, miyagun sun kai wannan harin ne, ƴan sa’oi baya tawagar kwamishinan ƴansanda na su wuce, hakan na nuna cewa, kodai dama, ƴan bindigar ba su taki sa’a bane, a lokacin harin na su ko kuma wani da masaniyar, daidai lokacin da suka tsara, kai harin na su.

LABARAI MASU NASABA

Gasar Kofin Duniya: Ko Morocco Na Iya Tsallake Tarkon Faransa?

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

Bugu da ƙarin, maharani sun kuma sake karkata akalarsu zuwa jihar Kebbi, inda suka kutsa cikin makarantar ƴan mata ta gwamnati da ke a garin Maga, suka yi awon gaba da ƴan mata 25, waɗanda wasunsu, ƴan shekaru 13 ne, tare da hallaka wani jami’in makarantar mai suna Hassan Makuku.

A yankin Arewa ta Tsakiya ma, haka batun yake, inda maharani suka kutsa cikin Cocin Christ Apostolic da ke a yankin Eruku,  na jihar Kwara, suna ta faman ruwan ruwan Albarusai, ba ƙaƙƙautawa, a yayin da mahalarta Cocin, ke kan gudanar da ibada, suka hallaka aƙalla mabiya uku tare da sace Jagoran Cocin da kuma wasu mabiya.

Duk dai a jihar ta Kwara, wasu ƴan bindiga sun yi garkuwa da wasu manoman Shinkafa huɗu a yankin Edu.

Hakazalika, sun kai hari a  garin Sabon Birni na jihar Sokoto, suka hallaka wani Basarake tare da sace wasu mutane 15, cikinsu har da wasu mata huɗu tare da jariran da suke shayarwa.

A jihar Yobe kuwa, mayaƙan ISWAP, sun auka a wani ƙaramin ofishin ƴansanda da ke a Geidam,  suka kashe ɗansanda ɗaya suka kuma  bankawa wasu motocinsu na fatirol wuta.

Ita jihar Neja, ba ta sha ba, domin maharani, su aukawa makarantun St. Mary’s Catholic da ke a yankin in Agwara, suka sace ƙananan ɗalibai sama da 300 da malamai sha biyu.

Ko da yake dai, an ruwaito cewa, gwamnatin jihar ta fitar da wata sanarwar kafin kai harin na su ce, an samu bayanan sirri na matsalar tsaro a yankin.

 A nan, za mu iya cewa, ba wai batu ne, na samun rahoton barazanar tsaro a jihar ba, amma lamari ne, kawai, da ke nuna cewa, mahukunta a Arewacin ƙasar, sun gaza wajen tsaron rayuka da dukiyoyin alummar yankin.

Wannan ƙalubalen na ƙarauwar matsalar tsaron ce, ta tilasata shugaba Bola Tinubu ya dakatar da tafiyar da ya tsara yi zuwa wani babban taro a ƙasashen Afirka ta Kudu da Angola, musamman domin jiran bayanai daga hafsjoshin tsaron ƙasar.

Tinubu, ya bayar da umarnin da a ƙara tura jami’an tsaro zuwa yankin na Eruku tare da umartarsu, da su bankaɗo duk inda miyagun suke a ɓoye.

Kazalika, ya umarci ƙaramin ministan tsaro Bello Matawalle, da ya tare a jihar Kebbi, har sai an gano ɗaliban da aka sace.

Tinubu ya kuma bayar da umarnin, da a rufe ɗaukacin makarantun sakantare na haɗaka 47, na ƙasar, wanda ya danganta wannan matakin saboda matslar ta tasaro.

Wannan matakin ya nuna a zahiri cewa, gwamnatin ba za ta iya kare rayukan ɗaliban ba

Tabbas, muna buƙatar a lalubo da mafita kan matsalar ta rashin tsaro, musamman duba da cewa, duk da irin yawan jami’an tsaron da ƙasar ke da su, amma gwamnatin, ta gaza kare rayukan ɗaliban.

Alamar tambayar a nan shi ne, rufe makarantun da tura ɗaliban gida shi ne mafita, bayan cewar, wasu alumomin da ɗaliban suka fito na ci gaba da fama da hare-haren ƴan bindiga?

Darun sojin mu, na mutuwa a fagen daga, ana kuma sace ɗalibai, yan bindiga na kai hare-hare a Coci-Coci, manoma a gonakansu, ba su tsira ba, manyan hanyoyi na ci gaba da zama tarkon mutuwa ga matafiya.

Ya zama wani,  kar shugaba Tinubu yayi sako-sako da wannan ƙalubalen, domin akwai buƙatar ayyana dokar ta ɓaci kan lamarin.

A bisa wannan matsalar ce, ƙasar Amurka ta ayyana Nijeriya a matsayin ƙasar da ya wajaba a mayar da hankali kan ƙalubalen rashin tsaro da rashin bai wa ƴan ƙasar ƴancin yin addini.

Wasu na yin hasashen cewa, ci gaba da samun tashe-tsahen hankula a ƙasar, na da nasaba da yunƙurin yiwa Tinubu zagon ƙasa domin kar gwamnatinsa ta wuce zuwa wa’adi na biyu.

Kazalika, akwai buƙatar a cafko waɗanda ake gani a ƙasar, sun eke ɗaukar nauyin ayyukan ta’addamci ko wanne irin matsayi na siyasa, suke riƙe da shi.

Hakazalika, akwai buƙatar a dakatar da duk wasu manyan taruka na siyasa, kuma a jingine batun duk wani lissafai, na yaya za a lashe zaɓen 2027.

Bisa wannan matsalar, tabbasa ba mu riga Malam Masallaci ba, idan muka ce, Nijeriya a yanzu, na cikin yaƙi ne kuma abin tambayar a nan shi ne, shi shugaban Tinibu,  gwamnatinsa a shirye take ta fara yaƙar matsalar matsalar tsaron da ta zamo wa ƙasar ƙarfan ƙafa?

Maraba
Ra'ayinmu
+ postsBio
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Kisan Gillar Marabar Jos: Bai Kamata Jinin Malama Ummulkhairi Ya Tafi A Banza Ba
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan
  • Ra'ayinmu
    https://hausa.leadership.ng/author/raayinmu/
    Ce-ce-ku-ce Kan Batun Biyan Bashin Naira Tiriliyan 3.3 Na Kuɗin Lantarki

MASU ALAKA

Gasar Kofin Duniya: Ko Morocco Na Iya Tsallake Tarkon Faransa?
Manyan Labarai

Gasar Kofin Duniya: Ko Morocco Na Iya Tsallake Tarkon Faransa?

July 5, 2026
Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC
Manyan Labarai

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

July 4, 2026
Kano Pillars Ta Naɗa Mataimakin Kocin Super Eagles, Daniel Ogunmodede A Matsayin Sabon Kocinta
Manyan Labarai

Kano Pillars Ta Naɗa Mataimakin Kocin Super Eagles, Daniel Ogunmodede A Matsayin Sabon Kocinta

July 3, 2026
Next Post
Ƴansanda Sun Fara Tabbatar Da Dokar Hana Zirga-zigar Babura A Kano

Ƴansanda Sun Fara Tabbatar Da Dokar Hana Zirga-zigar Babura A Kano

LABARAI MASU NASABA

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

July 5, 2026
Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

July 5, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

July 5, 2026
An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

July 5, 2026
Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

July 5, 2026
Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

July 5, 2026
Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

July 5, 2026
Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

July 5, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

July 5, 2026
Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo

July 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.