Masu ‘yan ta’adda da suka yi garkuwa da yaran gidan marayu da makaranta da ke wani yanki mai nisa a Zariagi, kusa da mahadar Kabba da ke Lokoja a Karamar Hukumar Lokoja ta Jihar Kogi, sun bukaci a biya su kudin fansa kimanin naira miliyan 150, kafin su saki yaran.
Lamarin, wanda ya faru a daren ranar Lahadin da ta gabata, an yi garkuwa da mutane kimanin 26 da suka hada da yara 24 da kuma mata biyu na mai gidan da suka shiga, a lokacin da wasu dauke da makamai suka kutsa kai cikin gidan.
Wani malami a makarantar, Isah Hajarat ya shaida wa wakilinmu cewa; an fara kai harin ne da misalin karfe 11:00 na dare, lamarin da ya jefa yankin cikin rudani.
“Wasu daga cikin yaran, sun yi nasarar tserewa a yayin harin, amma har yanzu mutum tara suna hannun wadanda suka sace sun,” in ji ta. “Masu garkuwa da mutanen, sun tuntubi mai gidan tare da neman kudin fansa kimanin naira miliyan 150.”
Daya daga cikin daliban da suka tsere, Faruk Alhassan, ya bayyana yadda lamarin ya faru, inda ya bayyana yadda suka samu kansu cikin firgici lokacin da ‘yan bindigar suka far wa harabar.
“Lokacin da suka zo, sai muka fara ihu da gudu domin mu samu mu tsira, wasu daga cikinmu, sun buya a daya daga cikin dakunan gidan, amma sai suka bi mu har can suka yi kokarin daukar kanina, inda nan take muka fara kuka,” in ji shi.
Faruk ya kara da cewa, daga baya Allah ya taimake shi ya samu ya gudu cikin daji, inda ya tuntubi mahaifinsa, shi kuma ya sanar da jami’an tsaro.
Duk da cewa, bai iya tantance maharan a fili ba, amma ya lura cewa; wasu daga cikinsu sun rufe fuskokinsu, dauke da manyan bindigogi da sauran muggan makamai.
Har ila yau, ya kuma yi kira ga gwamnati, da ta kara kaimi wajen ganin an ceto wadanda aka yi garkuwar da su.
Da yake tabbatar da faruwar lamarin, kwamishinan ‘yansanda na Jihar Kogi, CP Naziru Bello Kankarofi, ya ce; an kubutar da mutane 17 daga cikin wadanda aka sacen ta hanyar yin hadin gwiwa da jami’an tsaro da mafarauta da kuma ’yan banga.
“Mutanenmu sun samu kiran waya da misalin karfe 11:45 na rana, kuma nan take suka garzaya zuwa wurin, muna aiki tare da kungiyoyin tsaro na yankin, mun kuma samu nasarar ceto mutane 17 da lamarin ya rutsa da su, yayin da wasu da suka hada da matan mai gidan biyu da wasu ‘ya’yansa, har yanzu ba a samu damar kubutar da su ba,” in ji shi.
Kwamishinan ‘yansandan ya kara da cewa, ana nan ana ci gaba da gudanar da aikin hadin gwiwa tsakanin jami’an ‘yansanda, sojoji, mafarauta da kuma kungiyoyin ‘yan banga, domin ganin an kubutar da sauran wadanda harin ya rutsa da su.
Haka zalika, Kankarofi, ya nuna damuwarsa game da matakan tsaro na wajen, tare da lura da cewa; yankin da aka sace wadannan mutane, yanki ne mai nisa da yake a kebe, sannan kuma babu ingantaccen tsaro.
“Makarantar tana cikin wani yanki mai nisa da dazuzzuka, sannan babu hanyar shiga, babu kuma isassun gine-gine a wurin.













Discussion about this post