ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu Garkuwa Na Neman Naira Miliyan 150 Kan Yaran Da Suka Sace A Kogi

by Sani Anwar
2 months ago
Kogi

Masu ‘yan ta’adda da suka yi garkuwa da yaran gidan marayu da makaranta da ke wani yanki mai nisa a Zariagi, kusa da mahadar Kabba da ke Lokoja a Karamar Hukumar Lokoja ta Jihar Kogi, sun bukaci a biya su kudin fansa kimanin naira miliyan 150, kafin su saki yaran.

Lamarin, wanda ya faru a daren ranar Lahadin da ta gabata, an yi garkuwa da mutane kimanin 26 da suka hada da yara 24 da kuma mata biyu na mai gidan da suka shiga, a lokacin da wasu dauke da makamai suka kutsa kai cikin gidan.

Wani malami a makarantar, Isah Hajarat ya shaida wa wakilinmu cewa; an fara kai harin ne da misalin karfe 11:00 na dare, lamarin da ya jefa yankin cikin rudani.

ADVERTISEMENT

“Wasu daga cikin yaran, sun yi nasarar tserewa a yayin harin, amma har yanzu mutum tara suna hannun wadanda suka sace sun,” in ji ta. “Masu garkuwa da mutanen, sun tuntubi mai gidan tare da neman kudin fansa kimanin naira miliyan 150.”

Daya daga cikin daliban da suka tsere, Faruk Alhassan, ya bayyana yadda lamarin ya faru, inda ya bayyana yadda suka samu kansu cikin firgici lokacin da ‘yan bindigar suka far wa harabar.

LABARAI MASU NASABA

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

“Lokacin da suka zo, sai muka fara ihu da gudu domin mu samu mu tsira, wasu daga cikinmu, sun buya a daya daga cikin dakunan gidan, amma sai suka bi mu har can suka yi kokarin daukar kanina, inda nan take muka fara kuka,” in ji shi.

Faruk ya kara da cewa, daga baya Allah ya taimake shi ya samu ya gudu cikin daji, inda ya tuntubi mahaifinsa, shi kuma ya sanar da jami’an tsaro.

Duk da cewa, bai iya tantance maharan a fili ba, amma ya lura cewa; wasu daga cikinsu sun rufe fuskokinsu, dauke da manyan bindigogi da sauran muggan makamai.

Har ila yau, ya kuma yi kira ga gwamnati, da ta kara kaimi wajen ganin an ceto wadanda aka yi garkuwar da su.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, kwamishinan ‘yansanda na Jihar Kogi, CP Naziru Bello Kankarofi, ya ce; an kubutar da mutane 17 daga cikin wadanda aka sacen ta hanyar yin hadin gwiwa da jami’an tsaro da mafarauta da kuma ’yan banga.

“Mutanenmu sun samu kiran waya da misalin karfe 11:45 na rana, kuma nan take suka garzaya zuwa wurin, muna aiki tare da kungiyoyin tsaro na yankin, mun kuma samu nasarar ceto mutane 17 da lamarin ya rutsa da su, yayin da wasu da suka hada da matan mai gidan biyu da wasu ‘ya’yansa, har yanzu ba a samu damar kubutar da su ba,” in ji shi.

Kwamishinan ‘yansandan ya kara da cewa, ana nan ana ci gaba da gudanar da aikin hadin gwiwa tsakanin jami’an ‘yansanda, sojoji, mafarauta da kuma kungiyoyin ‘yan banga, domin ganin an kubutar da sauran wadanda harin ya rutsa da su.

Haka zalika, Kankarofi, ya nuna damuwarsa game da matakan tsaro na wajen, tare da lura da cewa; yankin da aka sace wadannan mutane, yanki ne mai nisa da yake a kebe, sannan kuma babu ingantaccen tsaro.

“Makarantar tana cikin wani yanki mai nisa da dazuzzuka, sannan babu hanyar shiga, babu kuma isassun gine-gine a wurin.

Kogi
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Gwamnati Ta Amince Da Inganta Cibiyar Kula Da Saran Maciji A Gwambe
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Hukumar NDLEA Ta Lalata Sama Da Tan 12 Na Miyagun Ƙwayoyi A Kano
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Labarai

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

July 7, 2026
'yansanda
Labarai

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

July 7, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Nuna Damuwa Kan Yawaitar Hare-haren Da Ake Kai Wa Jami’an Soji

July 7, 2026
Next Post
ADC Ta Fara Sayar Da Fom Din Takara Kafin Babban Taron Jam’iyya

Zaɓukan Fidda Gwani: ADC Ta Buƙaci INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

LABARAI MASU NASABA

Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

July 7, 2026
Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

July 7, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

July 7, 2026
Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

July 7, 2026
Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

July 7, 2026
Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

July 7, 2026
'yansanda

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

July 7, 2026
Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

July 7, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Nuna Damuwa Kan Yawaitar Hare-haren Da Ake Kai Wa Jami’an Soji

July 7, 2026
Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

July 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.