ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu Garkuwa Na Neman Naira Miliyan 150 Kan Yaran Da Suka Sace A Kogi

by Sani Anwar
1 month ago
Kogi

Masu ‘yan ta’adda da suka yi garkuwa da yaran gidan marayu da makaranta da ke wani yanki mai nisa a Zariagi, kusa da mahadar Kabba da ke Lokoja a Karamar Hukumar Lokoja ta Jihar Kogi, sun bukaci a biya su kudin fansa kimanin naira miliyan 150, kafin su saki yaran.

Lamarin, wanda ya faru a daren ranar Lahadin da ta gabata, an yi garkuwa da mutane kimanin 26 da suka hada da yara 24 da kuma mata biyu na mai gidan da suka shiga, a lokacin da wasu dauke da makamai suka kutsa kai cikin gidan.

Wani malami a makarantar, Isah Hajarat ya shaida wa wakilinmu cewa; an fara kai harin ne da misalin karfe 11:00 na dare, lamarin da ya jefa yankin cikin rudani.

ADVERTISEMENT

“Wasu daga cikin yaran, sun yi nasarar tserewa a yayin harin, amma har yanzu mutum tara suna hannun wadanda suka sace sun,” in ji ta. “Masu garkuwa da mutanen, sun tuntubi mai gidan tare da neman kudin fansa kimanin naira miliyan 150.”

Daya daga cikin daliban da suka tsere, Faruk Alhassan, ya bayyana yadda lamarin ya faru, inda ya bayyana yadda suka samu kansu cikin firgici lokacin da ‘yan bindigar suka far wa harabar.

LABARAI MASU NASABA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

“Lokacin da suka zo, sai muka fara ihu da gudu domin mu samu mu tsira, wasu daga cikinmu, sun buya a daya daga cikin dakunan gidan, amma sai suka bi mu har can suka yi kokarin daukar kanina, inda nan take muka fara kuka,” in ji shi.

Faruk ya kara da cewa, daga baya Allah ya taimake shi ya samu ya gudu cikin daji, inda ya tuntubi mahaifinsa, shi kuma ya sanar da jami’an tsaro.

Duk da cewa, bai iya tantance maharan a fili ba, amma ya lura cewa; wasu daga cikinsu sun rufe fuskokinsu, dauke da manyan bindigogi da sauran muggan makamai.

Har ila yau, ya kuma yi kira ga gwamnati, da ta kara kaimi wajen ganin an ceto wadanda aka yi garkuwar da su.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, kwamishinan ‘yansanda na Jihar Kogi, CP Naziru Bello Kankarofi, ya ce; an kubutar da mutane 17 daga cikin wadanda aka sacen ta hanyar yin hadin gwiwa da jami’an tsaro da mafarauta da kuma ’yan banga.

“Mutanenmu sun samu kiran waya da misalin karfe 11:45 na rana, kuma nan take suka garzaya zuwa wurin, muna aiki tare da kungiyoyin tsaro na yankin, mun kuma samu nasarar ceto mutane 17 da lamarin ya rutsa da su, yayin da wasu da suka hada da matan mai gidan biyu da wasu ‘ya’yansa, har yanzu ba a samu damar kubutar da su ba,” in ji shi.

Kwamishinan ‘yansandan ya kara da cewa, ana nan ana ci gaba da gudanar da aikin hadin gwiwa tsakanin jami’an ‘yansanda, sojoji, mafarauta da kuma kungiyoyin ‘yan banga, domin ganin an kubutar da sauran wadanda harin ya rutsa da su.

Haka zalika, Kankarofi, ya nuna damuwarsa game da matakan tsaro na wajen, tare da lura da cewa; yankin da aka sace wadannan mutane, yanki ne mai nisa da yake a kebe, sannan kuma babu ingantaccen tsaro.

“Makarantar tana cikin wani yanki mai nisa da dazuzzuka, sannan babu hanyar shiga, babu kuma isassun gine-gine a wurin.

Kogi
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tinubu Ya Jinjina Wa Jami’an Tsaro Kan Jajircewarsu Wajen Kawo Karshen Ta’addanci

MASU ALAKA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Rahotonni

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Labarai

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
Next Post
ADC Ta Fara Sayar Da Fom Din Takara Kafin Babban Taron Jam’iyya

Zaɓukan Fidda Gwani: ADC Ta Buƙaci INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.