ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Masu Ruwa Da Tsaki A APC Sun Bukaci Zulum Ya Zama Abokin Takarar Tinubu

Masu Ruwa Da Tsaki A APC Sun Bukaci Zulum Ya Zama Abokin Takarar Tinubu

by Sadiq
4 years ago
Zulum

Masu ruwa da tsaki a jam’iyyar APC sun yi kira ga shugabannin jam’iyyar da shugaban kasa Muhammadu Buhari da su dauki gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum a matsayin wanda zai yi wa Bola Ahmed Tinubu takarar mataimaki a zaben 2023.

Gamayyar masu ruwa da tsakin su 840, sun yi imanin cewa idan aka dauki Zulum za ta taimaka wa jam’iyyar wajen samun nasara a babban zabe mai zuwa na 2023, tare da taimakawa a kokarin ceto kasar nan daga durkushewa.

  • Farashin Gas Din Girki Ya Kara Yin Tashin Gwauron Zabi — NBS
  • Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Sule Da Sanata Jika Sun Fice Daga Jam’iyyar APC

Shugaban kungiyar na kasa, Abdullahi Aliyu Katsina, a lokacin da yake jawabi ga shugabannin jihohi bakwai na Arewa maso Yamma a Jihar Katsina a ranar Lahadi, ya bayyana cewa Zulum ne kadai wanda ya sace zukatan ‘yan Nijeriya ta hanyar jagoranci nagari a cikin shekaru uku da suka wuce.

ADVERTISEMENT

A cewarsa sadaukarwar da gwamna Zulum ya yi a Jihar Borno, ta isa jam’iyyar APC ta ba shi damar hidimtawa Nijeriya.

Har wa yau, ya ce ya yi imanin Zulum ne wanda ya fi dacewa da gurbin takarar mataimakin shugaban kasa.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

“Bukatar mu a bude take kuma bai wuce daukar gwamna Zulum na Jihar Borno a matsayin mataimakin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC ba.

“Mun fahimci cewa gwamna Zulum ne kadai zai iya kawo kuri’u daga jihohin Arewa 19.

“Don gudun kada a fadi zabe, a yau mutum daya tilo a Nijeriya wanda zai iya kawo wa jam’iyyar nan nasarar da ake bukata shi ne gwamna Zulum. Duk wanda a yau aka zaba a matsayin mataimakin shugaban kasa a jam’iyyar APC, in ba Zulum ba, ba zai iya kai mu ga gaci ba.

“Rashin zabar Zulum, zai iya kai mu ga faduwa zabe.”

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
Nasarar Oyebanji Ta Jadadda Yadda Ake Son APC — Buhari

Nasarar Oyebanji Ta Jadadda Yadda Ake Son APC — Buhari

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.