ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matasa 16 Masu Shirin Fara NYSC Sun Rasu A Mummunan Hatsarin Mota

by Abubakar Sulaiman
10 months ago
Matasa

Aƙalla matasa 16 ne daga cikin waɗanda suka kammala karatu a jami’ar ilimi ta Adeyemi (AFUED), dake jihar Ondo suka rasa rayukansu a wani mummunan hatsarin mota mai muni yayin da suke kan hanyar zuwa sansanin horaswa na NYSC da ke jihar Gombe. Lamarin ya faru ne a safiyar Litinin, inda rahotanni suka tabbatar cewa mutum biyu kacal suka tsira, amma suna cikin mummunan yanayi a asibiti.

Shaidun gani da ido yayin hatsarin sun bayyana cewa motar haya ƙirar bas mai kujeru 18 ce ta yi taho-mu-gama a hatsarin, wanda ya janyo lalacewar motocin  tare da haddasa munanan raunuka ga waɗanda suka tsira. Jami’an ceto sun isa wurin cikin gaggawa, tare  da ɗaukar gawarwaki da miƙa wadanda suka jikkata zuwa asibiti mafi kusa domin kulawa ta gaggawa.

  • ’Yansanda Sun Kama Ɗan Fashi Sanye Da Kayan NYSC A Enugu
  • Kamala Harris Za Ta Bayyana Mataimakin Takararta Kafin Shiga Zaben Amurka 

A halin yanzu, hukumar NYSC ba ta fitar da wata sanarwa ba kan abin da ya faru, yayin da Hukumar Kiyayeb Haɗurra ta ƙasa (FRSC) ta fara bincike don gano musabbabin haɗarin da ya jefa iyalai da al’ummar jami’ar cikin alhini. Lamarin ya sake cefa tambayoyi kan lafiyar hanyoyinmu da kuma yanayin lafiyar motocin hayar da ake amfani da su wajen jigilar mutane zuwa ko’ina cikin ƙasar.

ADVERTISEMENT

Jama’a da dama sun nuna damuwa a shafukan sada zumunta, inda malamai da ɗalibai da tsoffin ƴan NYSC ke kira ga gwamnati da hukumar NYSC su sake fasalin tsarin tura sabbin masu hidimar ƙasa, musamman wajen rage doguwar tafiya da ke jefa rayukan matasa cikin haɗari.

Wasu na ganin lokaci ya yi da za a kafa ƙa’idoji mafi tsauri kan motocin da ake haya da su don  jigilar sabbin masu yin hidimar ƙasa, tare da samar da ƙarin hanyar tafiya da tafi aminci.

LABARAI MASU NASABA

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Matasa
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Iyalin El-Rufai Sun Bai Ministan Tsaro Wa’adin Kwana 7 Kan Zargin Rikicin Kudancin Kaduna
  • Abubakar Sulaiman
    Atiku Ya Zargi Gwamnatin Tarayya Da Cin Bashi Kamar Mashayin Da Kuɗi Ya Ƙarewa
  • Abubakar Sulaiman
    Boko Haram Ta Kai Hari Adamawa, Ana Fargabar Mutuwar Mutane 11
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Sokoto, Sun Kashe Mutane 7, Sun Yi Garkuwa Da 12

MASU ALAKA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Next Post
Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Hada Karfi Tare Da Kasashe Masu Tasowa Wajen Kare Moriyar Bai Daya

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Hada Karfi Tare Da Kasashe Masu Tasowa Wajen Kare Moriyar Bai Daya

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.