Madarasatu Ummul Kura Islamiyya Garki Abuja, ta gabatar da walimar saukar Kur’ani daliban da suka samu saukar Alkur’ani Mai Girma karo na shida da makarantar ke yi a duk shekara, inda a wannan shekara dalibai 46 ne suka yi saukar maza bakwai Mata 39.
Da yake gabatar da jawabi a yayin taron Sarkin Garki Alhaji Dakta Usman, ya ja hankalin iyayen yara da su ba da himma wajen kula da karatun addinin ‘ya’yansu musamman ta wajen biya musu kudin makaranta, ya kuma roke su da su tallafa wa makarantar wanda ta haka ne ilimin ‘ya’yansu zai inganta.
Shi ma a nasa jawabin Sheikh Muhammad Nura Usman, ya yi kira ga iyayen yara ne da su kula da amanar da Allah ya danka a hannunsu, inda ya ce, kowa a ranar lahira sai an tambaye shi kiwon da aka bashi.
Sannan ya yi kira ga yara masu shagalyuwa da kalle-kallen kwallon kafa da su koma makaranta domin samun abin da zai cece su duniya da lahirarsu.
Haka shi ma Asarkin Samarin Garki Hausa Shugaban Matasa na Garki Gana Daya, Alhaji Abdulwahhab Musa, ya yi nuni da cewa, ilimin addini abu da dake taimakawa wajen gyara tarbiyyar matasa da kuma yara ta yadda suke tasowa da kyakkyawar tarbiyya, inda ya ce rashin kyakkyawar tarbiyya ce ke haifar da aikata miyagun laifuka kamar su: Satar mutane, ta’addanci da sauran miyagun ayyuka.
Ya ce hanyoyin dakile irin wadannan miyagun hala su ne a samu tarbiyya tun daga gida, inda ya ce ya kamata iyaye su rika sani abokan ‘ya’yansu, inda suka je da kuma ina za su je, ta haka ne za a samu ingantacciyar tarbiyya ga yara.
A nasa jawabin, Babban Limamin Juma’a na Garki Malam Abdullahi, addu’a ya yi gab akin da suka halarci taro da fatan alheri.Malam Mu’awiya Idris, shi ne shugaban wannan makanta ta Madarasau Ummul Kura Islamiyya Garki Abuja, ya yi LEADERSHIP bayanin farin cikin da yake yi, inda ya ce “Wannan rana ce ta farin ciki wanda ba zai misultu ba, saboda duk sanda aka ce ka karantar da dalibai har suka sauke Kur’ani a wurinka, wannan ba karamin abin farin ciki bane, domin duk sand aka koyar da wani akin alheri to duk sanda ya yi wannan aikin kana da lada.
”Ya yi kira ga iyayen yara da su bai wa ilimin addinin Musulunci muhimmanci ta hanyar kula da karatunsu.A cewarsa “Wannan ita ce hanya daya da rage wajen yi wa yara tarbiyya da kuma mayar da su masu kyakkyawar gobe, domin yana da kyau yadda iyaye ke ba wa bangaren Boko muhimmanci wannan shi ma a bashi hakan.
Taron dai ya samu halatar manyan baki irin su, Birgediya Janar Nura Muhammad, Sakin Garki Alhaji Usman, sai kuma Hakimin Hausawan Garki, Alhaji Umar Abubukar, da Iyan Misau Alhaji Sale Adamu, da Wamban Garki Alhaji Muhammad Rabiu, Santalin Garki Alhaji Isyaku Muhammad, da Sarikin Samarin Garki, Alhaji Abdulwahhab Musa, sai kuma zababben Kasilan Garki Hon. Alkasim Bala Sarki, da kuma Alhaji Muhammad Yunusa sarkin Fawan Garki da dai sauransu.















Discussion about this post