ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ummul Kura Islamiyya Garki Abuja, Ta Gudanar Da Walimar Saukar Kur’anin Ɗalibai

by Sulaiman and Rabi'u Ali Indabawa
3 months ago
Garki

Madarasatu Ummul Kura Islamiyya Garki Abuja, ta gabatar da walimar saukar Kur’ani daliban da suka samu saukar Alkur’ani Mai Girma karo na shida da makarantar ke yi a duk shekara, inda a wannan shekara dalibai 46 ne suka yi saukar maza bakwai Mata 39.

Da yake gabatar da jawabi a yayin taron Sarkin Garki Alhaji Dakta Usman, ya ja hankalin iyayen yara da su ba da himma wajen kula da karatun addinin ‘ya’yansu musamman ta wajen biya musu kudin makaranta, ya kuma roke su da su tallafa wa makarantar wanda ta haka ne ilimin ‘ya’yansu zai inganta.

Shi ma a nasa jawabin Sheikh Muhammad Nura Usman, ya yi kira ga iyayen yara ne da su kula da amanar da Allah ya danka a hannunsu, inda ya ce, kowa a ranar lahira sai an tambaye shi kiwon da aka bashi.

ADVERTISEMENT

Sannan ya yi kira ga yara masu shagalyuwa da kalle-kallen kwallon kafa da su koma makaranta domin samun abin da zai cece su duniya da lahirarsu.

Haka shi ma Asarkin Samarin Garki Hausa Shugaban Matasa na Garki Gana Daya, Alhaji Abdulwahhab Musa, ya yi nuni da cewa, ilimin addini abu da dake taimakawa wajen gyara tarbiyyar matasa da kuma yara ta yadda suke tasowa da kyakkyawar tarbiyya, inda ya ce rashin kyakkyawar tarbiyya ce ke haifar da aikata miyagun laifuka kamar su: Satar mutane, ta’addanci da sauran miyagun ayyuka.

LABARAI MASU NASABA

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

Ya ce hanyoyin dakile irin wadannan miyagun hala su ne a samu tarbiyya tun daga gida, inda ya ce ya kamata iyaye su rika sani abokan ‘ya’yansu, inda suka je da kuma ina za su je, ta haka ne za a samu ingantacciyar tarbiyya ga yara.

A nasa jawabin, Babban Limamin Juma’a na Garki Malam Abdullahi, addu’a ya yi gab akin da suka halarci taro da fatan alheri.Malam Mu’awiya Idris, shi ne shugaban wannan makanta ta Madarasau Ummul Kura Islamiyya Garki Abuja, ya yi LEADERSHIP bayanin farin cikin da yake yi, inda ya ce “Wannan rana ce ta farin ciki wanda ba zai misultu ba, saboda duk sanda aka ce ka karantar da dalibai har suka sauke Kur’ani a wurinka, wannan ba karamin abin farin ciki bane, domin duk sand aka koyar da wani akin alheri to duk sanda ya yi wannan aikin kana da lada.

”Ya yi kira ga iyayen yara da su bai wa ilimin addinin Musulunci muhimmanci ta hanyar kula da karatunsu.A cewarsa “Wannan ita ce hanya daya da rage wajen yi wa yara tarbiyya da kuma mayar da su masu kyakkyawar gobe, domin yana da kyau yadda iyaye ke ba wa bangaren Boko muhimmanci wannan shi ma a bashi hakan.

Taron dai ya samu halatar manyan baki irin su, Birgediya Janar Nura Muhammad, Sakin Garki Alhaji Usman, sai kuma Hakimin Hausawan Garki, Alhaji Umar Abubukar, da Iyan Misau Alhaji Sale Adamu, da Wamban Garki Alhaji Muhammad Rabiu, Santalin Garki Alhaji Isyaku Muhammad, da Sarikin Samarin Garki, Alhaji Abdulwahhab Musa, sai kuma zababben Kasilan Garki Hon. Alkasim Bala Sarki, da kuma Alhaji Muhammad Yunusa sarkin Fawan Garki da dai sauransu.

Garki
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku
  • Sulaiman
    Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives
  • Sulaiman
    Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong
  • Sulaiman
    Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana
Garki
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Birtaniya Ta Yaba Wa Tinubu Kan Sauye-sauyen Tattalin Arziki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Kungiya Ta Nemi Mambobinta Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihohi 28 Da Abuja Na Fuskantar Hadarin Ambaliyar Ruwa —Rahoto
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Jami’an Tsaro Suka Fatattaki ’Yan Ta’adda A Wasu Jihohin Nijeriya, Sun Kama ‘Yan Kasar Pakistan Bakwai

MASU ALAKA

Garki
Manyan Labarai

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Garki
Labarai

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

July 26, 2026
Garki
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Alƙalin Babbar Kotu A Kebbi

July 26, 2026
Next Post
Dangote Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Gaggauta Don Kawar Da Zazzabin Cizon Sauro

Dangote Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Gaggauta Don Kawar Da Zazzabin Cizon Sauro

LABARAI MASU NASABA

Garki

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

July 26, 2026
Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

July 26, 2026
Garki

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

July 26, 2026
Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

July 26, 2026
Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

July 26, 2026
Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

July 26, 2026
Garki

Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Alƙalin Babbar Kotu A Kebbi

July 26, 2026
Bala Mohammed

Sadakin Budurwa ₦3,000 Na Bazawara ₦1,500: Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaryata Batun

July 26, 2026
Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

July 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.