ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalolin Bashin Da Ake Bin Nijeriya

by Aminu Nasir
4 years ago
Nijeriya

A makonnin da suka gabata ne, ministan kudi da kasafi da tsare-tsaren kasa, Zainab Ahmed ta bayar da sanarwar cewa gwamnatin tarayya tana tunanin samun naira tiriliyan 8.5 a shekara ta 2023.

Idan muka yi la’akari da yanayin barayin mai da rashin tsaro da matsalolin tattalin arzikin duniya, za a iya cewa wannan hasashe na tattalin arziki ba daidai ba ne.

  • Tagomashin Da CBN Ya Samar Wajen Bunkasa Kanana Da Matsakaitan Sana’o’i

Muna fatan ‘yan majalisa za su mayar da hankalinsu sosai wajen duba wannan lamari na hasashe.

ADVERTISEMENT

Duk da cewa mafi yawansu ba za su dawo kujerarsu ba, kenan wannan ne damarsu ta karshe. Ya kamata su yi abin da za a yaba masu ko za a rika tuna su a tarihi mai kyau.

Gwamnatin da Shugaban kasa Muhammadu Buhari ke jagoranta watanni kadan ne ya rage mata kafin ta hannata wa sabuwar gwamnatin da ta sami nasara a zaben 2023. Batun gaskiya ba za a iya gane ainihin yanayin tattalin arzikin Nijeriya ba har sai bayan wannan gwamnatin da muke ciki a halin yanzu ta shude.

LABARAI MASU NASABA

Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1

Su Wa Ke Fatattakar Obi Da Kwankwaso?

Haka kuma, ministan ta fitar da daftarin cewa za a kashe naira tiriliyan 19.8, wanda shi ne ma kasafin kudi mafi yawa a tarihin Nijeriya.

Bayanai na nuna cewa gwamnati na bukatar bashin naira tiriliyan 11.3 don cike gibin kasafin kudi na shekara ta 2023. Wannan makudan kudade shi ne babban abun damuwar da kowa ya kamata hankalinsa ya koma kai.

A gaba daya gwamnati na samun kudaden kasafin kudinta na shekara daga kudaden shigarta ne. wadanda suka hada da haraji da sauran kasuwancin da gwamnati take yi kamar sayar da danyen mai na Nijeriya.

Kasashe da suke samun rara a kasafin kudinsu su ne wadanda suke kashe kudadensu kasa da kudaden shigarsu. Lokaci na karshe da Nijeriya ta sami rara a akasafin kudinta shi ne 2003, 2004 da 2005.

A duk lokacin da kudaden shiga suka gaza, kasa za ta iya nemo bashi don ta yi abubuwan da suka wajaba a kanta.
A batun gaskiya ‘yan kasa ba sa son gwamnatinsu ta rika karbo bashi ba dubawa. Ba wai hujja ba ne a ce kasashe irin su Amurka ko Japan ko Germany ko Butaniya suna amso bashi. Abun damuwar ita ce mutane da dama sun fahimci cewa gwamnati ba ta yin abubuwan da suka dace da kudaden da take amsowa.

A halin da ake ciki yanzu haka, Nijeriya tana kashe dukkanin kudaden shigarta a wajen biyan bashi ne, kuma matsalar ga al’umma ba a san yaushe za a warware wannan matsalar bashin ba. Mutane suna son su rika kwatanta bashin kasa da kasa kamar bashin wata kungiya ko magidanta.

Abun fa ba haka ba ne. Kasashe ba kasuwanci daya suke yi ba a tsakaninsu, kowacce kasa tana da kudadenta da dokokinta da yadda take karbar haraji da yadda take gudanar da harkokin kasuwancinta.

A zahiri matsalar kudade kasa ba zai iya kasancewa ana da isasshen kudaden da za su iya ba, amma kasa za ta iya warware matsalar bashinta saboda matsalolli da ka iya tasowa ba tare da isassun kudade ba, kamar abun da muka gani a Rasha kwanan nan.

Yanayin tattalin da kuma daidaitonsa ba za a iya biyan bashin da ake bin Nijeriya ba har sai an bi wadansu dokoki biyu, wanda ga bayaninsu ta yadda kowa ma zai iya fahimtarsu duk da yake ba kai-tsaye suke ba.

Na farko, kaddara cewa kudaden da ake sa ran samu suna daidai da bashin da ake bi, sai dauki kudin ruwa kai-tsaye zuwa asusun ajiya. A hasashen kudin da kasa ta yi ba za a iya biyan bashin da ake bin ta ba da wuri.

Na biyu, kasar a yanayin da take ciki na tattalin arziki ba za ta iya karbo bashi ta biya bashi da shi ba. Dokar kamar tsarin nan na Stopcok da ke cikin Ponzi Game. Ponzi game yananayi ne da kasa za ta karbo bashi ta biya wadanda ta karbo bashi a wurinsu. Bashin da ake karba kullum karuwa suke yi saboda kudin ruwan da suke cikinsu.

A bisa yanayin kididdigan da ake da su, bashin da ake bin Nijeriya da ke karuwa duk shekara a shekarar 2022 ya kai akalla kashi 4 cikin 100 kasa da yadda aka aro a shekarar 2021.

A maimakon kasar ta aro sama da kashi 40 wajen kashe kudade a shekarar 2022. Hakan na nuna cewa gwamnati ta ari naira 4 a kowacce naira 10 na kudaden shigar da ake samu, kuma ma har yanzu shekarar ba ta kare ba.

A saboda haka al’ummar kasa suna da damar da za su rika nuna damuwarsu kan yadda basussukan da ake bin Nijeriya ke kara hauhawa saboda babu wani shiri da zai iya saukar da wannan bashin da ake bin kasa.

Wajibi ne ‘yan majalisa su duba da idon basira don ganin sun tabbatar ana bin dokoki yadda suka dace ba. Wajibi ne majalisun kasa su sake duba dokokin yadda ake kashe kudade da kuma na babban bankin Nijeriya (CBN) tare da sanya doka da hukunta duk wanda ya karya doka, a kuma tabbata da samun mutanen da suka dace a kan kowani mukami.

Amma fa wannan ga shugabannin majalisar dattawa da wakiali masu zuwa, domin wadannan an zo bakin kofa.

Dakta Nasir Aminu
Dr. Nasir Aminu, Malami ne a Jami’ar Cardiff Metropolitan University da ke Birtaniya

Nijeriya
Aminu Nasir
+ postsBio
  • Aminu Nasir
    https://hausa.leadership.ng/author/aminu-nasir/
    Bashin Dala Miliyan 350 Da Kaduna Ta Ciyo: Nasara Ko Akasinta?
  • Aminu Nasir
    https://hausa.leadership.ng/author/aminu-nasir/
    Ko Ayyana Goyon Baya Ga Dan Siyasa Da Wasu Ke Yi Zai Yi Tasiri?
  • Aminu Nasir
    https://hausa.leadership.ng/author/aminu-nasir/
    Man Kolmani: Yaushe Za A Fara Cin Moriyarsa?
  • Aminu Nasir
    https://hausa.leadership.ng/author/aminu-nasir/
    Rudananin Sauya Fasalin Naira

MASU ALAKA

Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
Bakon Marubuci

Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1

May 27, 2026
obi
Bakon Marubuci

Su Wa Ke Fatattakar Obi Da Kwankwaso?

May 16, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Bakon Marubuci

Hanyoyin Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuradiyyar Nijeriya

May 10, 2026
Next Post
Sin Ta Yanke Shawarar Sanya Takunkumai A Kan Shugabannin Kamfanonin Amurka Da Ke Da Hannun Sayar Da Makamai ga Taiwan

Sin Ta Yanke Shawarar Sanya Takunkumai A Kan Shugabannin Kamfanonin Amurka Da Ke Da Hannun Sayar Da Makamai ga Taiwan

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.