ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsin Canjin Kudi Da Karancin Mai, Ko Kilu Za Ta Jawo Bau A APC?

by Yusuf Shuaibu
3 years ago

A yayin da ya rage saura kasa da mako biyu a gudanar da zaben shugaban kasa na 2023, ‘yan Nijeriya suna fuskantar matsin canjin kudi da man fetur a karkashin gwamnatin da jam’iyyar APC take jagoranta.

Idan za a iya tunawa a watan Nuwambar 2022, an samu dogayen layuka a gidajen mai a fadin kasar nan sakamakon rashin samun man fetur a wasu gidajen mai, yayin da wadanda ke da man suka sayar da nasu a kan naira 240, wanda ya karu da naira 85 a farashin da kamfanin main a kasa (NNPC) ya amince a kan a sayar da man kan naira 165.

  • Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Inganta Bude Kofarta Ba Tare Da Yin Kasa A Gwiwa Ba

Kungiyar dillalan man fetur mai zaman kanta ta Nijeriya (IPMAN) ta danganta karin farashin da aka samu kan karin kudin man a rubun sayar da man daga naira 148 zuwa 200 kan kowacce lita.

ADVERTISEMENT

A cewar shugaban gudanarwa na kungiyar IPMAN, Mike Osatuyi “Ba kamar yadda a baya ‘ya’yan kungiyarmu ke sayan man kan naira 148 kan kowacce lit aba, a halin yanzu suna sayan kowacce lita kan naira 200. Ba zai yi wuya su sayar da man fetur a kan naira 165 kan kowacce lita kamar yadda aka kayyade.

“A halin yanzu mambobin kungiyarmu suna matukar shan wahala wajen samun man. Haka kuma ‘yan kasuwan suna kashe makudan kudade wajen kai man zuwa sassa daban-daban na kasar nan saboda tsadar man dizil, inda a halin yanzu ana sayar da kowacce lita daya ta dizil kan naira 800.

LABARAI MASU NASABA

Makarantu Za Su Ci Gaba Da Zama A Rufe Har Sai Yanayin Tsaro Ya Inganta – Gwamnatin Kebbi

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda Takwas A Katsina

Duk da kiraye-kirayen da bangarori daban-daban suke yi ciki har da majalisar dokokin ta kasa da ‘yan kasuwan man fetur ga NNPC na magance matsalar man fetur, farashin man ya ci gaba da karuwa tun a watan Nuwambar 2022, kuma a halin yanzu ana sayar da man tsakanin naira 240 zuwa naira 500 kan kowacce lita guda.

A hannu guda kuma, ‘yan Nijeriya ba su farfado daga matsalar karancin man fetur ba, sai babban bankin Nijeriya (CBN) ya sauya fasalin kudi tare da bayar da wa’adin ranar 31 ga Junairu za a daina amsar tsofaffin takardun kudi na naira 200, 500 da kuma 1,000.

CBN ya sanar da shirin sake fasalin wasu takardun kudaden ne a ranar 26 ga Oktoban 2022, da nufin rage hauhawar farashin kayayyaki da hana fasa kwaurin kudin banki da kuma rage zirga-zirgan kudade.
A ranar 23 ga watan Nuwamban 2022, Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kaddamar da sabbin takardun kudade, wanda aka gabatar wa jama’a a ranar 15 ga Disambar 2022.

Kwanaki kadan gabanin wa’adin farko na ranar 31 ga Janairu ya kare, an ga jerin layuka a na’urar cire kudi (ATIM) na bankuna daban-daban da ke Nijeriya wajen neman cire kudin sabbin kudade, yayin da wasu bankunan suke rufe na’urar ATM dinsu saboda dalilin cire kude.

Rashin fitar da sabbin takardun kudade da bankuna ke kin yi ya sa lamarin ya kara ta’azzara, domin a cewar rahotanni, da yawa daga cikinsu sun ci gaba da fitar da tsofaffin takardun kudaden ta na’urar ATM kuma tsawan makonni da fitowar sabbin kudaden ba a bayar da su a cikin bankuna.

Duk da tsawaita wa’adin daina amsar tsofaffin takardun kudaden da CBN ya yi da kwanaki 10 tare da bayar da umurni ga bankuna kan yadda za a samar da sabbin takardun kudaden da aka sauya wa fasali ga ‘yan Nijeriya, amma al’umma kasar nan na cikin firgici saboda rashin isassun sabbin kudaden a hannun jama’a.
“Zan iya bayyana muku cewa kullum CBN ya bai wa bankuna sabbin kudade. Kamar yadda nake magana a halin yanzu, bankuna sun amshi sabbin kudade daga CBN.

“Ina tabbatar muku da cewa muna rokon bankuna kasuwanci da su zo su karbi sabbin kudade daga CBN. Muna da wadannan sabbin takardun kudade a rumbun ajiyarmu, kuma muna jiran bankuna su zo su karbe su,” in ji Daraktan sashen shari’a na CBN, Mista Kofo Salam-Alada, a wani shirin wayar da kan jama’a na kauyen Kwamfuta da ke Ikeja a Jihar Legas a ranar 19 ga Janairu.
Rashin samun sabbin kudaden ya yi matukar illata harkokin kasuwanci, musamman ma bangaren da ake hada-hada da tsabar kudade wajen gudanar da harkokin kasuwanci.
Jam’iyyar APC tana ganin cewa an kawo wadannan tsarin ne domin a hana ta cin zabe.
Mai Magana da yawun dan takarar shugaban kasa na APC, Dakta Jose Onoh ya siffanta tsarin sauya takardun kudade da gwamnan CBN, Mista Godwin Emefiele ya kawo a matsayin huce haushi kan siyasa bayan da ya gaza samun tikitin takarar shugaban kasa.
Onog ya kara da cewa sake fasalin naira ba wai tsatin jam’iyyar APC ba ne, illa ce ta Emefiele wanda a halin yanzu ke kawo cikas ga tattalin arzikin kasa, inda ya bayar da shawarar cewa kasar ta yi koyi da tsarin kasar Ingila na canjin kudi a hankali har na tsawon watanni 12 a kalla.
Onoh ya jaddada cewa bai kamata a daidai lokacin zabe a sauya fasalin takardun kudade, kuma wannan muguwar manufar Emefiele na hukunta ‘yan Nijeriya saboda ya gaza samun takarar shugaban kasa.
Ya bayar da misalign irin tashin hankula da ‘yan Nijeriya suka fada sakamakon karancin kudade wadanda suka hada da zanga-zanga, sayar da sabbin kudade ba bisa ka’ida ba, tilastawan ‘yan ta’adda kan samun sabbin kudaden da kuma sauran matsaloli da suka shafi zamantakewa.
Ya ce abin takaici ne yadda gwamnatin Nijeriya ta nada wanda bai cancanta ya tafiyartar da harkokin kudade ba, kuma babban kuskure ne tun lokacin da gwamnan CBN ya shiga siyasa.
A cerwarsa, ko kadan bai kamata a bar Emefiele ya koma bakin aiki ba bayan ya gaza samun takarar shugaban kasa, yana jin haushin rashin nasara da ya yi wanda ya zabi ya huce haushinsa kan daukacin al’ummar Nijeriya.
Onoh ya yi gargadin cewa manufar sake fasalin kudin naira na CBN shi ne, ya haifar da tarzoma cikin jama’a, yana mai jaddada cewa ya kamata Emefiele ya bar ofis ne a daidai lokacin da ya nuna sha’awar zama dan takarar shugaban kasa.
A cikin makon da ya gabata ne, Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir el-Rufa’i ya bayyana cewa akwai wasu daga cikin fadar shugaban kasa suna yin kutungwila ga dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Ahmad Tinubu wajen ganin bai ci zaben 2023 ba.
El-Rufa’i ya bayyana hakan ne lokacin da yake fira da BBC Hausa, wanda ya ce sauya fasalin takardun kudi abu ne mai kyau amma bai kamata a gudanar da shi a daidai lokacimn da ake fusukantar zabe ba. Ya ce an yi hakan ne saboda a saka kiyayya a tsakanin ‘yan Nijeriya da jam’iyyar APC.
Sai dai kuma masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC sun goyi bayan gwamna el-Rufai na ikirarin akwai wadanda suke zagaye da Shugaban kasa Muhammadu Buhari da ba sa kaunar Tinubu.

Tun a shekarun da suka gabata ne, Uwargidan shugaban kasa, Aisha Buhari ta sanar wa ‘yan Nijeriya cewa akwai kabal a suka kewaye mijinta wadanda suka hana ruwa gudu.

Shugaban tawagar masu ruwa da tsaki na APC, Dominic Alancha ya tabbatar da cewa akwai wadansu mutane da ke kewaye da shugaban kasa suna hana ruwa gudu ga nasarar jam’iyyar.

Haka kuma Alancha ya zargi kwamitin gudanarwa na jam’iyyar kan kin bayyana wa sauran mambobin jam’iyyar bayanan kudade.

Alancha ya koka kan yadda ‘ya’yan jam’iyyarnke sauya sheka zuwa jam’iyyun adawa tun bayan zaben fitar da gwani na 2022, yayin da manyan masu ruwa da tdsaki suka yi watsi da su.
Masana harkokin siyasa suna ganin wadannan lamura za su iya kawo wa jam’iyyar APC cikas a zaben 2023. A mahangar masanan, matsin canjin kudi da karancin man fetur suna iya goga wa APC bakin jini na rasa magoya baya.

Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

MASU ALAKA

kebbi
Labarai

Makarantu Za Su Ci Gaba Da Zama A Rufe Har Sai Yanayin Tsaro Ya Inganta – Gwamnatin Kebbi

July 9, 2026
Ta’addanci
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda Takwas A Katsina

July 9, 2026
Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Next Post
Kamata Ya Yi A Daure Duk Dan Kasuwar Da Ke Shigo Da Tufafi Nijeriya Daga Kasar Waje —Dangote

Kamata Ya Yi A Daure Duk Dan Kasuwar Da Ke Shigo Da Tufafi Nijeriya Daga Kasar Waje —Dangote

LABARAI MASU NASABA

kebbi

Makarantu Za Su Ci Gaba Da Zama A Rufe Har Sai Yanayin Tsaro Ya Inganta – Gwamnatin Kebbi

July 9, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Shugabar Namibia

Li Qiang Ya Gana Da Shugabar Namibia

July 9, 2026
Xi Ya Bayar Da Umarni Dangane Da Gobarar Da Ta Tashi A Wani Kamfanin Sarrafa Takalma Dake Gabashin Kasar

Xi Ya Bayar Da Umarni Dangane Da Gobarar Da Ta Tashi A Wani Kamfanin Sarrafa Takalma Dake Gabashin Kasar

July 9, 2026
Ta’addanci

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda Takwas A Katsina

July 9, 2026
Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

July 9, 2026
Auto Draft

TCN Ta Kammala Gyaran Layin Wutar Lantarkin Zaria–Funtua 132kV

July 9, 2026
Auto Draft

DSS Ta Kama ‘Yar Jarida Zainab Sodiq Kan Zargin Mallakar Drone Ba Tare da Cikakkun Takardu ba

July 9, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji

July 9, 2026
Shaidar EFCC Ya Ce Sirika Bai Sanya Hannu A Takardun Kwangilar Naira Biliyan 2 Ba

Shaidar EFCC Ya Ce Sirika Bai Sanya Hannu A Takardun Kwangilar Naira Biliyan 2 Ba

July 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.