Mataimakiyar Sakatare-Janar ta Majalisar Ɗinkin Duniya, Amina Mohammed, ta sake jaddada aniyar ƙungiyar na tallafa wa hanyoyin da ƴan Nijeriya ke jagoranta wajen magance matsalolin ci gaba da na jin ƙai.
Mai magana da yawun Majalisar Ɗinkin Duniya, Stéphane Dujarric, ya ce Mohammed ta dawo daga Nijeriya a ranar Litinin, inda ta kai ziyara jihohin Zamfara da Binuwe, tare da ganawa da al’ummomin da rikice-rikice da gudun hijira suka shafa.
- Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
- Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
- An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
- Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
- Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030
Ya ce ta gani da idonta irin girman buƙatun jin ƙai da ake da su, tare da ƙoƙarin da gwamnati da abokan hulɗa ke yi domin taimakawa.
A wani ɓangare kuma, Majalisar Ɗinkin Duniya ta ce amfani da fasahar zamani na dijital na sauya yadda Nijeriya ke tunkarar matsalolin jin ƙai, ciki har da bibiyar ƴan gudun hijira a cikin gida, duk da ƙarancin kuɗi da kuma giɓin fasaha.
An bayyana hakan ne a yayin zaman taro na 59 na Hukumar Yawan Jama’a da Ci Gaba (CPD59) da ke gudana a hedikwatar Majalisar Ɗinkin Duniya a birnin New York.
Nijeriya, wadda ke da kusan mutum miliyan biyu da suka rasa matsugunansu sakamakon rikicin ƴan ta’adda a yankin Arewa maso Gabas, ta fara amfani da tsarin Displacement Tracking Matriɗ da International Organization for Migration ta ƙirƙira domin inganta tattara bayanai da kuma mayar da martani ga waɗannan matsaloli.
Majalisar Ɗinkin Duniya ta bayyana cewa wannan tsarin na taimaka wa yanke shawara a ƙasashe sama da 90, abin da ke nuna muhimmancin fasaha a tsara ci gaban ƙasa.
Sai dai kuma, ta yi gargaɗi kan wasu ƙalubale kamar rashin daidaito wajen samun fasahar dijital, barazanar sirrin bayanai, da kuma yaɗuwar labaran ƙarya, musamman ga al’umma masu rauni.
Babban Sakatare-Janar na Majalisar Ɗinkin Duniya, António Guterres, ya kuma nuna damuwa kan raguwar kuɗaɗen tallafi na duniya ga shirye-shiryen ci gaba, yana mai cewa adadin da ake bayarwa yanzu bai isa ba wajen cimma burin ci gaba mai ɗorewa.
Ya buƙaci a samar da ƙarin kuɗaɗe masu ƙarfi da tabbas, musamman ga ƙasashe masu rauni.
Kamfanin Dillancin Labaran Nijeriya (NAN) ya ruwaito cewa wannan kwamiti na nazarin yadda sauye-sauyen yawan jama’a ke tasiri ga ci gaba mai ɗorewa.














