ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

MDD Ta Nuna Goyon Bayanta Ga Tsarin Samar Da Ci Gaba Na Nijeriya

by Sani Anwar
2 months ago
NIJERIYA

Mataimakiyar Sakatare-Janar ta Majalisar Ɗinkin Duniya, Amina Mohammed, ta sake jaddada aniyar ƙungiyar na tallafa wa hanyoyin da ƴan Nijeriya ke jagoranta wajen magance matsalolin ci gaba da na jin ƙai.

Mai magana da yawun Majalisar Ɗinkin Duniya, Stéphane Dujarric, ya ce Mohammed ta dawo daga Nijeriya a ranar Litinin, inda ta kai ziyara jihohin Zamfara da Binuwe, tare da ganawa da al’ummomin da rikice-rikice da gudun hijira suka shafa.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Ya ce ta gani da idonta irin girman buƙatun jin ƙai da ake da su, tare da ƙoƙarin da gwamnati da abokan hulɗa ke yi domin taimakawa.

ADVERTISEMENT

A wani ɓangare kuma, Majalisar Ɗinkin Duniya ta ce amfani da fasahar zamani na dijital na sauya yadda Nijeriya ke tunkarar matsalolin jin ƙai, ciki har da bibiyar ƴan gudun hijira a cikin gida, duk da ƙarancin kuɗi da kuma giɓin fasaha.

An bayyana hakan ne a yayin zaman taro na 59 na Hukumar Yawan Jama’a da Ci Gaba (CPD59) da ke gudana a hedikwatar Majalisar Ɗinkin Duniya a birnin New York.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Nijeriya, wadda ke da kusan mutum miliyan biyu da suka rasa matsugunansu sakamakon rikicin ƴan ta’adda a yankin Arewa maso Gabas, ta fara amfani da tsarin Displacement Tracking Matriɗ da International Organization for Migration ta ƙirƙira domin inganta tattara bayanai da kuma mayar da martani ga waɗannan matsaloli.

Majalisar Ɗinkin Duniya ta bayyana cewa wannan tsarin na taimaka wa yanke shawara a ƙasashe sama da 90, abin da ke nuna muhimmancin fasaha a tsara ci gaban ƙasa.

Sai dai kuma, ta yi gargaɗi kan wasu ƙalubale kamar rashin daidaito wajen samun fasahar dijital, barazanar sirrin bayanai, da kuma yaɗuwar labaran ƙarya, musamman ga al’umma masu rauni.

Babban Sakatare-Janar na Majalisar Ɗinkin Duniya, António Guterres, ya kuma nuna damuwa kan raguwar kuɗaɗen tallafi na duniya ga shirye-shiryen ci gaba, yana mai cewa adadin da ake bayarwa yanzu bai isa ba wajen cimma burin ci gaba mai ɗorewa.

Ya buƙaci a samar da ƙarin kuɗaɗe masu ƙarfi da tabbas, musamman ga ƙasashe masu rauni.

Kamfanin Dillancin Labaran Nijeriya (NAN) ya ruwaito cewa wannan kwamiti na nazarin yadda sauye-sauyen yawan jama’a ke tasiri ga ci gaba mai ɗorewa.

NIJERIYA
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Sojoji Sun Ceto Mutum 92 Tare Da Daƙile Harin Ƴan Ta’adda A Borno
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Uzodimma: Babu Dimokraɗiyya Idan Babu Hamayya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Alamomin Fara Ruɓewar Hannu Bayan Ɗorin Gida
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ministocin Da Suka Ajiye Muƙamansu Ba Su Samu Tikitin Takara Ba

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Ma’aikatar Ilimi Ta Ce Za Ta Amfana Da Tallafin Dala Miliyan 552

Ma’aikatar Ilimi Ta Ce Za Ta Amfana Da Tallafin Dala Miliyan 552

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.