Ma’aikatar ilimi ta tarayya, tare da haɗin gwiwa da Hukumar ilimin bai ɗaya (UBEC), ta wayar da kan masu ruwa da tsaki na sassan Arewa maso yamma da Arewa maso gabas kan yadda za a aiwatar ta tsarin zuba tallafi na dala ,miliyan $552.18 domin bunƙasa ilimin bai ɗaya a Nijeriya.
Lamarin na wayar da kan an yi shi ne a Kano,ya kuma maida hankali ne kan su tsare- tsaren biyu wato HOPE-EDU da kuma HOPE-GOƁ, waɗanda Bankin Duniya da kuma wani tsarin haɗin gwiwa na duniya domin bunƙasa ilimi suka samar da kuɗaɗen (GPE), ba domin komai ba sai saboda, a bunƙasa lamarin ilimin bai ɗaya (UBE) a faɗin Nijeriya ko kuma kowane saƙo da lungu na ƙasar.
- NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund
- Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
- Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar
- Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili
- Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya
A wurin taron, babbar jami’a kuma Sakatariya ta Hukumar UBEC, Aisha Garba, ta bayyana cewa shi tsarin ya yi daidai da irin ,manufar Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu wato wani tsari ne da ya maida kan shi dangane da irin ratar da aka samu a tsari na na ilimin bai ɗaya a Nijeriya.
Ta ƙara bayyana cewa tsare- tsaren ana sa ran za su bunƙasa da kuma amfanar da yara milyan 29 da ake son su yadda suke koyo bayan an koya masu fahimtarsu da ganewa ta inganta, sai kuma taimakawa Malaman makaranta 500,000 domin bunƙasa rayuwarsu,ga kuma gina azuzuwa 13,000, domin a samu shawo kan matsalar yara waɗanda suka bar zuwa makaranta a faɗin Nijeriya baki ɗaya.
Garba ta ce yayin da ma’aikatar ilimi ta tarayya da Hukumar ilimin bai ɗaya za su samar da kuɗaɗen da kuma taimako na fasaha, su kuma gwamnatocin Jihohi sune za su aiwatar da tsarin a Jihohinsu.
“Nasarar da za a iya samu ashi wannan tsarin ya dogara ne kai aiwatar da lamarin da ya shafi gaskiya, riƙon amana, da kuma haɗin gwiwa da masu ruwa da tsaki. Dole ne Jihohi su kasance su ne masu aiwatar da abin ta hanyar tsari mafi dacewa, al’umma su kasance a ciki wajen aiwatarwar kamar yadda ta ce,”.
Ta yi kira da masu halartar taron cewar su yi amfani da duk abubuwan da suka dace domin su gano irin halin da ake ciki na maganar ci gaban da aka samu na aikin, da kuma ko ana kashe kuɗaɗen da kamar yadda da ce.
Shi ma a na shi jawabinin , Kwamishinan ilimi na Jihar Kano , Dakta Ali H. Abubakar Makoda, ya bayyana tsarin da ake son ɓullowa da shi a matsayin zai kasance a lokacin da ake son shi, don haka ne ya yi kira da Jihohi su tabbatar ana samun ci gaba da kuma nasara kan yadda ake koya ma ɗaliban da ko su kuma suna fahimtar abinda ake koya ma su.
Makoda ya ce Jihar Kano ta ba ilimi miuhimmanci ta hanyar ƙara kuɗaɗen da take yi,ɗaukar Malaman makaranta masu yawa, ƙara bunƙasa abubuwa da za su inganta jin daɗin koyarwa, abinda ake koya ma ɗalibai kuma su fahimce shi sosai,inda ya ce Jihar a shirye ta ke da ta aiwatar da tsarin HOPE-EDU a cikin tsarin kawo gyaran da take yi na ɓangaren ilimi.















Discussion about this post