ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mene Ne Sirrin Bunkasar Tattalin Arzikin Kasar Sin?

by Sulaiman and CGTN Hausa
4 months ago
Tattalin arziki

Aminanmu ’yan Afirka da yawa suna mamakin bunkasar tattalin arzikin kasar Sin, kuma sun sha tambaya cewa mene ne sirrin kasar wajen kiyaye ci gabanta? A ganina, Emmanuel Matambo, darektan cibiyar nazarin harkokin Afirka da kasar Sin da ke jami’ar Johannesburg ta kasar Afirka ta Kudu, ya ba da amsar tambayar daga wani muhimmin fanni, idan muka yi la’akari da furucin da ya yi ba da jimawa ba, inda ya ce, “Wani muhimmin dalilin da ya sa kasar Sin ta ke zama ginshikin bunkasar tattalin arzikin duniya, shi ne yadda take dukufa a kan samar da sabon karfin da ke tabbatar da ci gabanta”, kuma a hakika muna iya gano hakan daga rahoton aikin gwamnati da firaministan kasar Sin Li Qiang ya gabatar a yau.

Da safiyar yau Alhamis aka kaddamar da taron shekara-shekara na majalisar wakilan jama’ar kasar Sin, wadda ta kasance hukumar koli ta kasar, inda a madadin majalisar gudanarwar kasar, firaministan kasar Sin Li Qiang ya gabatar da rahoton aikin gwamnati, rahoton da ya shaida cewa, a shekarar 2025, kasar Sin ta yi ta raya sabon karfin samar da ci gabanta yadda ya kamata, kuma ta cimma gagaruman nasarori wajen kirkire-kirkiren kimiyya da fasaha, inda ta shiga sahun gaba ta fannonin nazarin fasahar kwaikwayon tunanin dan Adam, da harhada magunguna, da mutum-mutumin inji da kimiyyar “quantum” da sauransu.

“Sabon karfin da ke samar da ci gaban kasa” na nufin karfin da ake iya samu ta fannin bunkasa tattalin arziki ta hanyar hada fasahohin ci gaba da kuma sana’o’in gargajiya. A shagalin murnar bikin sabuwar shekarar gargajiya ta Sinawa da babban rukunin gidajen rediyo da talabijin(CMG) ya gabatar a kwanan baya, shirin yadda mutum-mutumin inji kirar kasar Sin ke wasan Kungfu ya burge masu kallo daga duk fadin duniya, wanda ya shaida babban ci gaban kasar ta fannin kimiyya da fasaha, musamman ma sabon karfin da ke iya samar da ci gaba a kasar.

ADVERTISEMENT

Ci gaban kimiyya da fasaha ba ya iya rabuwa da muhimmancin da gwamnati ta dora a fannin da ma tsare-tsaren da ta yi. A hakika, kullum kasar Sin na dora matukar muhimmanci a kan kirkire-kirkiren kimiyya da fasaha, idan mun yi la’akari da shirye-shiryenta na raya kasa na shekaru biyar biyar. Har wa yau, a shekarar 2025, kudaden da kasar Sin ta zuba ta fannin gudanar da ayyukan nazarin kimiyya da fasaha ya kai kudin Sin yuan triliyan 3 da biliyan 926. Idan kuma mun duba lokacin da aka aiwatar da shirin raya kasa na shekaru biyar biyar karo na 14, wato daga shekarar 2021 zuwa ta 2025, za mu gano cewa, yawan kudaden da aka zuba ya kiyaye matsakaicin karuwa da ya kai kaso 10% a kowace shekara.

A bana ne za a fara aiwatar da shirin raya kasa na shekaru biyar biyar karo na 15, kuma rahoton aikin gwamnati da aka gabatar a yau ya yi nuni da cewa, bisa ga daftarin shirin, kasar Sin za ta mai da hankali a kan tsayawa a kan kafafuwanta wajen raya kimiyya da fasaha, tare da inganta kirkire-kirkire da nazarin muhimman fasahohi na zamani, don ingiza gine-ginen kasar Sin na dijital, tare da fatan ganin karuwar kudin muhimman sana’o’i masu alaka da tattalin arziki na dijital ya kai kimanin kaso 12.5% na karuwar mizanin GDP na kasar baki daya.

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

Har ila yau, kirkire-kirkiren kimiyya da fasaha ya riga ya zama wani muhimmin bangare na hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka. Yadda kasar Sin za ta mai da hankalinta a kan raya sabon karfin samar da ci gabanta a yayin aiwatar da shirin raya kasa na shekaru biyar biyar karo na 15, zai kuma haifar da damammaki ga kasashen Afirka, da ma sauran kasashe masu tasowa a fadin duniya. Kamar yadda wakilin gidan talabijin na QTV na kasar Gambia, Ousman Jatta, wanda a halin yanzu ke ba da rahotannin taron da ke gudana a Beijing ya ce, “Kasar Sin na taimakawa kasashe masu tasowa wajen tabbatar da ci gabansu. Kasar Sin ta kasance mai kishin zaman lafiya, kuma tana kokarin bunkasa fasahohi, yanzu haka a kasar Sin, motocin lantarki da fasahar AI sun zama ruwan dare. A kasarmu kuma, an zamanantar da hidimomin motocin haya na Taxi zuwa salon dijital, haka kuma ana kokarin zamanantar da harkokin motocin lantarki zuwa salon na dijital. Ana aiwatar da gyare-gyare, duk da cewa ba cikin sauri ba. Muna sa ran mu ma za mu iya cimma burin raya kanmu kamar yadda kasar Sin ta yi.” Alal hakika, furucinsa ya bayyana burin kasashen Afirka da dama, wato yadda kasar Sin ke kokarin zamanantar da kanta, na samar da abin koyi, da kuma damar hadin gwiwa ga kasashen Afirka a kokarinsu na zamanantar da kansu.

Tattalin arziki
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
  • Sulaiman
    Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba
  • Sulaiman
    Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
  • Sulaiman
    Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje
Tattalin arziki
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

MASU ALAKA

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya
Ra'ayi Riga

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

June 19, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”
Ra'ayi Riga

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Daga Taklamakan Zuwa Sahara: Yadda Hamada Ke “Haifar” Da Fata
Ra'ayi Riga

Daga Taklamakan Zuwa Sahara: Yadda Hamada Ke “Haifar” Da Fata

June 17, 2026
Next Post
Darussa Daga Ramadan Na (1)

Darussa Daga Ramadan Na 13: Tsayuwar Dare

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.