ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mene Ne Sirrin Bunkasar Tattalin Arzikin Kasar Sin?

by Sulaiman and CGTN Hausa
3 months ago
Tattalin arziki

Aminanmu ’yan Afirka da yawa suna mamakin bunkasar tattalin arzikin kasar Sin, kuma sun sha tambaya cewa mene ne sirrin kasar wajen kiyaye ci gabanta? A ganina, Emmanuel Matambo, darektan cibiyar nazarin harkokin Afirka da kasar Sin da ke jami’ar Johannesburg ta kasar Afirka ta Kudu, ya ba da amsar tambayar daga wani muhimmin fanni, idan muka yi la’akari da furucin da ya yi ba da jimawa ba, inda ya ce, “Wani muhimmin dalilin da ya sa kasar Sin ta ke zama ginshikin bunkasar tattalin arzikin duniya, shi ne yadda take dukufa a kan samar da sabon karfin da ke tabbatar da ci gabanta”, kuma a hakika muna iya gano hakan daga rahoton aikin gwamnati da firaministan kasar Sin Li Qiang ya gabatar a yau.

Da safiyar yau Alhamis aka kaddamar da taron shekara-shekara na majalisar wakilan jama’ar kasar Sin, wadda ta kasance hukumar koli ta kasar, inda a madadin majalisar gudanarwar kasar, firaministan kasar Sin Li Qiang ya gabatar da rahoton aikin gwamnati, rahoton da ya shaida cewa, a shekarar 2025, kasar Sin ta yi ta raya sabon karfin samar da ci gabanta yadda ya kamata, kuma ta cimma gagaruman nasarori wajen kirkire-kirkiren kimiyya da fasaha, inda ta shiga sahun gaba ta fannonin nazarin fasahar kwaikwayon tunanin dan Adam, da harhada magunguna, da mutum-mutumin inji da kimiyyar “quantum” da sauransu.

“Sabon karfin da ke samar da ci gaban kasa” na nufin karfin da ake iya samu ta fannin bunkasa tattalin arziki ta hanyar hada fasahohin ci gaba da kuma sana’o’in gargajiya. A shagalin murnar bikin sabuwar shekarar gargajiya ta Sinawa da babban rukunin gidajen rediyo da talabijin(CMG) ya gabatar a kwanan baya, shirin yadda mutum-mutumin inji kirar kasar Sin ke wasan Kungfu ya burge masu kallo daga duk fadin duniya, wanda ya shaida babban ci gaban kasar ta fannin kimiyya da fasaha, musamman ma sabon karfin da ke iya samar da ci gaba a kasar.

ADVERTISEMENT

Ci gaban kimiyya da fasaha ba ya iya rabuwa da muhimmancin da gwamnati ta dora a fannin da ma tsare-tsaren da ta yi. A hakika, kullum kasar Sin na dora matukar muhimmanci a kan kirkire-kirkiren kimiyya da fasaha, idan mun yi la’akari da shirye-shiryenta na raya kasa na shekaru biyar biyar. Har wa yau, a shekarar 2025, kudaden da kasar Sin ta zuba ta fannin gudanar da ayyukan nazarin kimiyya da fasaha ya kai kudin Sin yuan triliyan 3 da biliyan 926. Idan kuma mun duba lokacin da aka aiwatar da shirin raya kasa na shekaru biyar biyar karo na 14, wato daga shekarar 2021 zuwa ta 2025, za mu gano cewa, yawan kudaden da aka zuba ya kiyaye matsakaicin karuwa da ya kai kaso 10% a kowace shekara.

A bana ne za a fara aiwatar da shirin raya kasa na shekaru biyar biyar karo na 15, kuma rahoton aikin gwamnati da aka gabatar a yau ya yi nuni da cewa, bisa ga daftarin shirin, kasar Sin za ta mai da hankali a kan tsayawa a kan kafafuwanta wajen raya kimiyya da fasaha, tare da inganta kirkire-kirkire da nazarin muhimman fasahohi na zamani, don ingiza gine-ginen kasar Sin na dijital, tare da fatan ganin karuwar kudin muhimman sana’o’i masu alaka da tattalin arziki na dijital ya kai kimanin kaso 12.5% na karuwar mizanin GDP na kasar baki daya.

LABARAI MASU NASABA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

Har ila yau, kirkire-kirkiren kimiyya da fasaha ya riga ya zama wani muhimmin bangare na hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka. Yadda kasar Sin za ta mai da hankalinta a kan raya sabon karfin samar da ci gabanta a yayin aiwatar da shirin raya kasa na shekaru biyar biyar karo na 15, zai kuma haifar da damammaki ga kasashen Afirka, da ma sauran kasashe masu tasowa a fadin duniya. Kamar yadda wakilin gidan talabijin na QTV na kasar Gambia, Ousman Jatta, wanda a halin yanzu ke ba da rahotannin taron da ke gudana a Beijing ya ce, “Kasar Sin na taimakawa kasashe masu tasowa wajen tabbatar da ci gabansu. Kasar Sin ta kasance mai kishin zaman lafiya, kuma tana kokarin bunkasa fasahohi, yanzu haka a kasar Sin, motocin lantarki da fasahar AI sun zama ruwan dare. A kasarmu kuma, an zamanantar da hidimomin motocin haya na Taxi zuwa salon dijital, haka kuma ana kokarin zamanantar da harkokin motocin lantarki zuwa salon na dijital. Ana aiwatar da gyare-gyare, duk da cewa ba cikin sauri ba. Muna sa ran mu ma za mu iya cimma burin raya kanmu kamar yadda kasar Sin ta yi.” Alal hakika, furucinsa ya bayyana burin kasashen Afirka da dama, wato yadda kasar Sin ke kokarin zamanantar da kanta, na samar da abin koyi, da kuma damar hadin gwiwa ga kasashen Afirka a kokarinsu na zamanantar da kansu.

Tattalin arziki
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Tattalin arziki
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

MASU ALAKA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki
Ra'ayi Riga

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

June 3, 2026
Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka
Ra'ayi Riga

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

June 1, 2026
Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya

May 29, 2026
Next Post
Darussa Daga Ramadan Na (1)

Darussa Daga Ramadan Na 13: Tsayuwar Dare

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.