Wasu ‘yan bindiga sun sace fasinjoji, ciki har da ɗaliban da za su rubuta jarabawar Jamb, bayan sun kai hari kan wata motar ‘Benue Links’ a hanyar Makurdi zuwa Otukpo a jihar Benue.
Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne da daddare, inda maharan suka tare motar ɗauke da kusan fasinjoji 18, suka yi awon gaba da mafi yawansu zuwa cikin daji, yayin da direba da wani fasinja suka tsere.
‘JAMB Ta Ce Laifi Ne Dalibi Ya Boye Matakin Karatun Da Yake’
Makafi 37 Sun Zana Jarabawar JAMB A Bauchi
Kwamishinan ‘yansandan jihar, Ifeanyi Emenari, ya tabbatar da cewa mutane 14 aka sace, yayin da mutum guda ya tsere, yana mai cewa yana jagorantar aikin ceto su a yankin Otukpo tare da jami’an tsaro.
Ya kuma bayyana cewa an fara bincike kan yadda lamarin ya faru, musamman ganin cewa kamfanin motar Benue Links na da dokar hana tafiya da daddare, amma ana zargin direban ya ɗauki fasinjojin ne bayan lokacin aiki.
Shi ma shugaban ƙaramar hukumar Otukpo, Maxwell Ogiri, ya tabbatar da aukuwar lamarin, yana mai cewa an tura jami’an tsaro zuwa dazuka domin ceto waɗanda aka sace, waɗanda yawancinsu matasa ne da ke kan hanyarsuu ta zuwa rubuta jarabawar JAMB.















Discussion about this post