ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministan Yaɗa Labarai Ya Gargaɗi Matasa Kan Yaɗa Labaran Ƙanzon Kurege

by Rabi'u Ali Indabawa
4 months ago
Ministan

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai na Ƙasa, Mohammed Idris, ya yi gargaɗin cewa yaɗa bayanan ƙarya na haifar da manyan ƙalubale na ɗabi’a da na ƙasa, tare da kira ga matasan Nijeriya da sauran ’yan ƙasa da su riƙa tantance gaskiyar duk wani bayani kafin su yaɗa shi.

Da yake jawabi a taron laccar Azumin Ramadan ta haɗin gwiwa karo na 20 da gidan talabijin na NTA, da Gidan Rediyon Faransa (FRCN) da Mutyar Nijeriya (ƁON) suka shirya a Kaduna jiya, ministan ya yi kashedin cewa rashin amfani da dandalin zamani yadda ya kamata na iya ƙara rarrabuwar kai tare da raunana haɗin kan ƙasa idan ba a tafiyar da su bisa alhaki da gaskiya ba.

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci Matasa Su Riƙa Tantance Sahihancin Labari Kafin Su Yaɗa Shi
  • Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang

Ministan ya jaddada cewa duk da cewa fasahar zamani ta dijital na kawo manyan damammaki, tana kuma tafe da jarabawar ɗabi’a da ke buƙatar ladabi da ɗaukar alhaki. Ya ƙara da cewa tabbatar da sahihancin bayanai ya zama wajibi na ɗan ƙasa da kuma na ɗabi’a.

ADVERTISEMENT

Haka kuma, ministan ya bayyana shirye-shiryen ƙarfafa matasa da dama a ƙarƙashin jagorancin Shugaba Bola Tinubu, waɗanda ke amfani da fasaha a matsayin hanya ta samar da damar tattalin arziki.

Ya lissafo tsare-tsare irin su shirin 3 Million Technical Talent (3MTT), da Asusun Lamunin Ilimi na Nijeriya (NELFUND), da kuma kafa cibiyar farko a Afirka ta Ilimin Kafofin Yaɗa Labarai da Ilimin Tantance Bayanai (Media and Information Literacy Institute).

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

A cewarsa, ilimin kafofin yaɗa labarai shi ne “rigakafin” yaɗa bayanan ƙarya, kuma waɗannan ƙoƙari an tsara su ne domin bai wa matasan Nijeriya ƙwarewar da za su buƙata domin samun nasara a tattalin arzikin dijital.

Ministan ya lura cewa yawan matasan da Nijeriya ke da su na ɗaya daga cikin manyan ƙarfinta, amma ya yi gargaɗin cewa makomar ƙasar na rataye ne kan yadda ake shiryawa da tallafa wa matasa yadda ya kamata.

“Ƙasar da ta gaza kula da matasanta ba ta da makoma. Muna zuba jari a tsari mai ɗorewa inda fasahar dijital za ta zama matakala ta samun dama,” in ji shi.

Ya kuma buƙaci matasan Nijeriya da su yi amfani da dandamalin dijital wajen ayyuka masu amfani kamar ilimi, ƙirƙire-ƙirƙire da ci gaban ƙasa.

“Ku tantance kafin ku yaɗa. Ku dakata. Ku binciki tushen labarin,” in ji shi, yana mai ƙarawa da cewa dole ne a yi amfani da kayan aikin dijital wajen ƙarfafa haɗin kai, ilimi da ci gaba maimakon haifar da rarrabuwar kai.

Ministan
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi
Labarai

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Next Post
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Tinubu Ya Tura Sabbin Jakadu 65 Zuwa Ƙasashe Daban-daban

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.