ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministan Yaɗa Labarai Ya Gargaɗi Matasa Kan Yaɗa Labaran Ƙanzon Kurege

by Rabi'u Ali Indabawa
6 months ago
Ministan

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai na Ƙasa, Mohammed Idris, ya yi gargaɗin cewa yaɗa bayanan ƙarya na haifar da manyan ƙalubale na ɗabi’a da na ƙasa, tare da kira ga matasan Nijeriya da sauran ’yan ƙasa da su riƙa tantance gaskiyar duk wani bayani kafin su yaɗa shi.

Da yake jawabi a taron laccar Azumin Ramadan ta haɗin gwiwa karo na 20 da gidan talabijin na NTA, da Gidan Rediyon Faransa (FRCN) da Mutyar Nijeriya (ƁON) suka shirya a Kaduna jiya, ministan ya yi kashedin cewa rashin amfani da dandalin zamani yadda ya kamata na iya ƙara rarrabuwar kai tare da raunana haɗin kan ƙasa idan ba a tafiyar da su bisa alhaki da gaskiya ba.

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci Matasa Su Riƙa Tantance Sahihancin Labari Kafin Su Yaɗa Shi
  • Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang

Ministan ya jaddada cewa duk da cewa fasahar zamani ta dijital na kawo manyan damammaki, tana kuma tafe da jarabawar ɗabi’a da ke buƙatar ladabi da ɗaukar alhaki. Ya ƙara da cewa tabbatar da sahihancin bayanai ya zama wajibi na ɗan ƙasa da kuma na ɗabi’a.

ADVERTISEMENT

Haka kuma, ministan ya bayyana shirye-shiryen ƙarfafa matasa da dama a ƙarƙashin jagorancin Shugaba Bola Tinubu, waɗanda ke amfani da fasaha a matsayin hanya ta samar da damar tattalin arziki.

Ya lissafo tsare-tsare irin su shirin 3 Million Technical Talent (3MTT), da Asusun Lamunin Ilimi na Nijeriya (NELFUND), da kuma kafa cibiyar farko a Afirka ta Ilimin Kafofin Yaɗa Labarai da Ilimin Tantance Bayanai (Media and Information Literacy Institute).

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

A cewarsa, ilimin kafofin yaɗa labarai shi ne “rigakafin” yaɗa bayanan ƙarya, kuma waɗannan ƙoƙari an tsara su ne domin bai wa matasan Nijeriya ƙwarewar da za su buƙata domin samun nasara a tattalin arzikin dijital.

Ministan ya lura cewa yawan matasan da Nijeriya ke da su na ɗaya daga cikin manyan ƙarfinta, amma ya yi gargaɗin cewa makomar ƙasar na rataye ne kan yadda ake shiryawa da tallafa wa matasa yadda ya kamata.

“Ƙasar da ta gaza kula da matasanta ba ta da makoma. Muna zuba jari a tsari mai ɗorewa inda fasahar dijital za ta zama matakala ta samun dama,” in ji shi.

Ya kuma buƙaci matasan Nijeriya da su yi amfani da dandamalin dijital wajen ayyuka masu amfani kamar ilimi, ƙirƙire-ƙirƙire da ci gaban ƙasa.

“Ku tantance kafin ku yaɗa. Ku dakata. Ku binciki tushen labarin,” in ji shi, yana mai ƙarawa da cewa dole ne a yi amfani da kayan aikin dijital wajen ƙarfafa haɗin kai, ilimi da ci gaba maimakon haifar da rarrabuwar kai.

Ministan
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas

MASU ALAKA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Next Post
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Tinubu Ya Tura Sabbin Jakadu 65 Zuwa Ƙasashe Daban-daban

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.