ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Munafunci Dodo Ya Kan Ci Mai Shi

by Sulaiman
6 months ago
Dodo

Katobarar da firaministar kasar Japan Takaichi Sanae ta yi a kwanakin baya, cewa wai “farmakin kasar Sin a kan Taiwan” na iya zama “barazana ga dorewar kasar Japan”, lamari ne da zai sa Japan ta dauki matakan soja, ya yi matukar fusata al’ummar kasar Sin, har ma gwamnatin kasar Sin ta dauki kwararan matakai na mayar da martani, don bayyana niyyarta a kan batun Taiwan, wato batun Taiwan ba na wasa ba ne, kuma duk wanda ya yi wasa da batun lallai zai kare a kansa.

Akwai aminaina ‘yan Nijeriya da suka min tambaya, cewa me ya sa kasar Sin ta mayar da martani mai karfin haka game da kalaman Takaichi Sanae? Domin amsa tambayar, zan so in tattauna tare da ku game da tarihin yankin Taiwan, da ma ainihin abun da ya haddasa batun Taiwan, da ma mugun burin da Takaichi Sanae ke neman cimmawa.

In mun yi nazari a kan tarihi da ma dokoki, za mu tabbatar da cewa, Taiwan wani yanki ne na kasar Sin. Muna iya gano sunan Taiwan a littattafan gargajiya na kasar Sin tun karni na 3. Tun karni na 12 kuma, gwamnatocin daulolin gargajiya na kasar Sin suka fara mulkin yankin Taiwan. A shekarar 1895, kasar Japan ta mamaye yankin Taiwan bisa yakin da ta tayar, daga nan kuma ta shafe tsawon shekaru 50 tana wa yankin mulkin mallaka, wanda ya zama tarihi mafi muni ga yankin Taiwan. Bayan yakin duniya na biyu, Sanarwar Cairo, da Sanarwar Potsdam, da takardar ba da kai ta Japan da dai sauran wasu takardu masu karfin doka na duniya, a bayyane ne suka bukaci Japan da ta mayar da Taiwan, da ma tsibiran Penghu da ta sata daga hannun kasar Sin. Ya zuwa ranar 25 ga watan Oktoban shekarar 1945, gwamnatin kasar Sin ta sanar da maido da mulki a yankin Taiwan, daga nan kuma, yankin Taiwan ya dawo karkashin mulkin kasar Sin bisa doka kuma a zahiri. Ba da jimawa ba bayan da kasar Sin ta cimma nasarar yaki da mamayar dakarun kasar Japan, jam’iyyar Kuomingtang da a wancan lokaci take mulki a kasar Sin ta tada yakin basasa, sai dai ba a kai shekaru uku ba ta ci tura, har ma ta gudu zuwa yankin Taiwan. Kasar Amurka ta nuna goyon baya ga jam’iyyar Kuomingtang, ta hanyar hana rundunar sojojin ‘yantar da jama’ar kasar Sin su ‘yantar da yankin Taiwan, lamarin da kuma ya haifar da batun Taiwan da muke fuskanta a yau. Duk da matsalar siyasa da babban yankin kasar Sin, da kuma yankin Taiwan suka fuskanta a cikin sama da shekaru 70 da suka wuce, ba a taba raba Taiwan daga kasar Sin ba, kuma kasancewar yankin Taiwan wani bangare ne na kasar Sin abu ne na zahiri wanda ba a taba canza shi ba.

ADVERTISEMENT

To, da haka muke iya gano cewa, katobarar Takaichi Sanae ta kasance tsoma baki cikin harkokin gida na kasar Sin, wadda kuma ta lalata dokokin kasa da kasa, da ma tsarin odar duniya bayan yakin duniya na biyu.

Ga wadanda za su iya tunawa da tarihi, sun san ba wannan ne karon farko da Japan ta yi amfani da kalmar “barazanar dorewar kasa”, da “kare kai”, wajen kaddamar da munanan farmakin soji ba. A cikin shekarar 1931, Japan ta bayyana “ko za a samu iko a yankin Manchuria na kasar Sin” a matsayin abin da ke “barazana ga dorewar kasa”, har ma ta fara kai hari ga yankin arewa maso gabashin kasar Sin, daga nan har ta fadada yaki zuwa sauran sassan Asiya. Har wa yau, Japan ta kuma taba kallon “ko za a kai hari tashar ruwa ta Pearl Harbour ko a’a”, a matsayin “abin da ke barazana ga dorewar kasa”, lamarin da daga baya ta haddasa yakin tekun Pasifik. A yau kuma, firaministar kasar Japan ta sake ambaton batun “barazana ga dorewar kasa”, ke nan me take neman cimmawa? Ko tana son maimaita abubuwan da suka faru a tarihi, tare da sake yin gaba da jama’ar kasar Sin da na Asiya baki daya? Ko kuma tana fatan ganin an lalata tsarin odar duniya bayan yakin duniya na biyu?

LABARAI MASU NASABA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

Bana ake cika shekaru 80 da samun nasarar yakin da al’ummar Sin suka yi da mamayar dakarun kasar Japan, da yakin kin tafarkin murdiya a duniya, haka kuma ake cika shekaru 80 da kasar Sin ta dawo da yankin Taiwan daga mulkin mallaka na kasar Japan. Kasar Sin za ta tsaya tsayin daka a kan hana farfadowar ra’ayin nuna karfin soja, tare da kiyaye nasarorin da aka cimma a yakin duniya na biyu, da ma tsarin odar duniya bayan yakin. Kamata ya yi sassan kasa da kasa su ma su hada hannu wajen kiyaye zaman lafiya da kwanciyar hankali a duniya. Japan a nata bangaren, ya kamata ta martaba zaman lafiya a maimakon yin watsi da tarihi. (Lubabatu)

Dodo
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • Sulaiman
    ’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

MASU ALAKA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki
Ra'ayi Riga

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

June 3, 2026
Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka
Ra'ayi Riga

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

June 1, 2026
Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya

May 29, 2026
Next Post
Ɗalibai 50 Da Aka Sace A Neja Sun Tsere CAN

Ɗalibai 50 Da Aka Sace A Neja Sun Tsere CAN

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.