ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 19, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ɗalibai 50 Da Aka Sace A Neja Sun Tsere CAN

by Abubakar Sulaiman
8 months ago
Ɗalibai

LABARAI MASU NASABA

Damawa Da Mata A Siyasa: Kujerun Majalisun Tarayya Na Iya Ƙaruwa Zuwa 121, da Kuma 397 A 2027

Abubuwa Uku Da Ya Kamata Kusani Akan Kofin Duniya

Ƙungiyar Kiristoci ta Nijeriya (CAN) reshen Jihar Neja ta tabbatar da cewa ɗalibai 50 daga cikin waɗanda aka sace daga Makarantar Sakandare da Firamare ta St. Mary’s, Papiri, a ƙaramar hukumar Agwara, sun tsere daga hannun waɗanda suka yi garkuwa da su. Hare-haren dai sun faru ne da safiyar Juma’a, inda maharan suka kashe ɗan banga sannan suka yi awon gaba da sama da mutane 200, ciki har da malamai 13.

A rahotonsa na farko, Shugaban CAN na Jihar Neja, Most Rev. Bulus Dauwa Yohanna, wanda shi ne mai makarantar, ya ce an sace ɗalibai 215 tare da malamai 12. Sai dai daga baya, a ranar Asabar, ya bayyana cewa an gano cewa wasu ƙarin dalibai 88  sun ɓace bayan sake yin ƙididdiga. A sanarwar da mai taimaka masa, Daniel Atori, ya fitar a madadinsa a ranar Lahadi, ya tabbatar da cewa ɗalibai 50 sun samu damar tserewa kuma sun haɗu da iyayensu.

  • Adadin Ɗaliban Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja Ya Kai 315 – CAN
  • Gwamnan Neja Ya Yi Allah-Wadai Da Sace Ɗaliban St. Mary A Papiri

Rev. Yohanna ya bayyana cewa makarantar na da tsarin kwana da na zuwa gida, inda 377 daga cikin ɗalibai 430 na firamare ke zaune a makarantar, yayin da 53 ke zuwa daga gida. Ya ce a halin yanzu, baya ga waɗanda suka tsere, ɗalibai 141 ba su shiga cikin waɗanda aka sace ba, yayin da ɗalibai 236, yara guda uku ƴaƴan ma’aikata, da ɗaliban sakandare 14 da ma’aikata 12 ke hannun masu garkuwa.

ADVERTISEMENT

Hukumomin tsaro dai sun ce suna ƙara ƙaimi wajen ganin sun ceto sauran mutanen da ke hannun maharan.

Ɗalibai
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Abubuwa Shida Da Ya Kamata Mace Ta Sani Kafin Ta Yi Aure
  • Abubakar Sulaiman
    Sabon Tsarin Tikitin Abinci Na Nusuk Zai Iya Ƙara Kuɗin Bizar Umrah
  • Abubakar Sulaiman
    Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu
  • Abubakar Sulaiman
    Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

MASU ALAKA

majalisar kasa
Manyan Labarai

Damawa Da Mata A Siyasa: Kujerun Majalisun Tarayya Na Iya Ƙaruwa Zuwa 121, da Kuma 397 A 2027

July 19, 2026
Kofin Duniya
Wasanni

Abubuwa Uku Da Ya Kamata Kusani Akan Kofin Duniya

July 19, 2026
Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna
Rahotonni

Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna

July 18, 2026
Next Post
Taron G20 Ya Nuna Makomar Duniya Mai Haske

Taron G20 Ya Nuna Makomar Duniya Mai Haske

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Tinubu Zai Yi Jawabi Ga Shugabannin Duniya A Taron MDD Karo Na 81

Shugaba Tinubu Zai Yi Jawabi Ga Shugabannin Duniya A Taron MDD Karo Na 81

July 19, 2026
majalisar kasa

Damawa Da Mata A Siyasa: Kujerun Majalisun Tarayya Na Iya Ƙaruwa Zuwa 121, da Kuma 397 A 2027

July 19, 2026
Kofin Duniya

Abubuwa Uku Da Ya Kamata Kusani Akan Kofin Duniya

July 19, 2026
Ɗalibai

Abubuwa Shida Da Ya Kamata Mace Ta Sani Kafin Ta Yi Aure

July 19, 2026
An Kaddamar Da “Bikin Fasahar AI Na Sin Na 2026” A Shanghai

An Kaddamar Da “Bikin Fasahar AI Na Sin Na 2026” A Shanghai

July 18, 2026
Fim Ko Gaske:Yaushe Masu Kallon Fina-finai Za Su Daina Daukar Fim A Matsayin Gaske

Fim Ko Gaske:Yaushe Masu Kallon Fina-finai Za Su Daina Daukar Fim A Matsayin Gaske

July 18, 2026
Sin Ta Nuna Matukar Adawa Da Matakin Burtaniya Na Mallake Kamfanin Karafa Na British Steel

Sin Ta Nuna Matukar Adawa Da Matakin Burtaniya Na Mallake Kamfanin Karafa Na British Steel

July 18, 2026
Tasirin AI (Artificial Intelligence) A Harkokin Al’umma Na Yau Da Kullum

Tasirin AI (Artificial Intelligence) A Harkokin Al’umma Na Yau Da Kullum

July 18, 2026
Xavi Ya Ce A Shirye Yake Ya Karɓi Ragamar Horar Da Tawagar Ƙasa

Xavi Ya Ce A Shirye Yake Ya Karɓi Ragamar Horar Da Tawagar Ƙasa

July 18, 2026
Masanin Kimiyya Na Sin Ya Lashe Kyautar UNESCO-Russia Mendeleev A Fannin Tushen Kimiyya

Masanin Kimiyya Na Sin Ya Lashe Kyautar UNESCO-Russia Mendeleev A Fannin Tushen Kimiyya

July 18, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.