ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutane Sun Fara Tona Ramin Tururuwa Don Neman Abinci A Borno

by Sadiq
2 years ago
Tururuwa

Mata masu shayarwa da kananan yara a Jihar Borno, sun fara bin gidan tururuwa suna neman abinci, sakamakon ta’azzarar rashin abinci da karuwar cutar tamowa.

Mazauna wasu yankuna a Jihar Borno da ma’aikatan kiwon lafiya, sun shiga damuwa game da karuwar yara masu tamowa a jihar.

  • Jami’ar Franco-British International Ta Shirya Soma Aiki A Watan Oktoba – Shugaban Jami’ar
  • Gwamnati Ta Janye Dokar Hana Fita A Kaduna Da Zariya 

Abin da suka ce na da nasaba da rashin wadataccen abinci mai gina jiki ga mata masu shayarwa.

ADVERTISEMENT

Bugu da kari rahotanni sun nuna cewa kananan hukumomi bakwai ne a jihar ta Borno, matsalar ta fi shafa.

Kananan hukumomin sun hada da Marte da Kukawa da Abadam da Guzamala da Kaga da Mobar da kuma Gubio.

LABARAI MASU NASABA

Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

EFCC Ta Cafke Lauyan Bogi Da Mallakar Hatimin Kungiyar Lauyoyi Ta Nijeriya Na Jabu A Legas

Yaran da ke a wadannan yankuna sun dogara ne da tallafin da suke samu daga kungiyoyin agaji.

Wata mata da ke aiki a kungiyoyin agaji, Fatima Muhammed Habib, ta manema labarai cewa, a da mutane ba su san ana fama da wannan matsala ba.

”Da muka je daya daga cikin wadannan yankuna mun tarar rabin yaran garin na fama da matsalar abinci mai gina jiki, haka suma matan da ke shayarwa, za ka gan su duk a wahale babu wani abinci mai maiko ko kyau da suke samu suna ci ga shi kuma suna shayarwa.”

Ta ce idan har uwa ba ta ci ta koshi ba ta yaya za ta samu ruwan nono bare har ta shayar da danta?

“Saboda tsananin yunwa haka za ka ga mata na tona gidan tururuwa don samu abinci, haka mata ke kungiya suna yawo don neman gidan tururuwar da za su samu abinci.”

“Babban abin tashin hankali shi ne daji matan ke zuwa don su samo gidan tururuwar, ga rashin tsaro a wuraren ga macizai da dai sauransu.”

Ta ce suna kai musu taimako, amma taimakon ba lallai ya isa ba.

Cutar tamowa dai ta jima ana yaki da ita, musamman a yankunan Arewacin Nijeriya.

MASU ALAKA

Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa
Al'ajabi

Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

June 9, 2026
EFCC Ta Cafke Lauyan Bogi Da Mallakar Hatimin Kungiyar Lauyoyi Ta Nijeriya Na Jabu A Legas
Al'ajabi

EFCC Ta Cafke Lauyan Bogi Da Mallakar Hatimin Kungiyar Lauyoyi Ta Nijeriya Na Jabu A Legas

April 21, 2026
Yadda Aka Gano Ƙasusuwan Dabba Mai Shekara Miliyan 100 A Nijar
Al'ajabi

Yadda Aka Gano Ƙasusuwan Dabba Mai Shekara Miliyan 100 A Nijar

March 8, 2026
Next Post
Ambaliyar Ruwa Ta Raba Hanyar Bauchi Zuwa Kano

Ambaliyar Ruwa Ta Raba Hanyar Bauchi Zuwa Kano

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 30, Sun Ƙone Gidaje Da Shaguna A Kaduna 

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 30, Sun Ƙone Gidaje Da Shaguna A Kaduna 

July 27, 2026
Kwalejin Kimiyya Ta Kogi Ta Dakatar Da Malamai Kan Zargin Lalata Da Ɗalibai Da Sauran Laifuka

Kwalejin Kimiyya Ta Kogi Ta Dakatar Da Malamai Kan Zargin Lalata Da Ɗalibai Da Sauran Laifuka

July 27, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

Kuri’u Za Su Yi Tasiri A Zaɓen 2027, In Ji INEC

July 27, 2026
Auto Draft

ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa

July 27, 2026
Tururuwa

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

July 26, 2026
Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

July 26, 2026
Tururuwa

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

July 26, 2026
Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

July 26, 2026
Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

July 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.