ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutum 146,913 Za Su Sa Ido A Zaben 2023 –INEC

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
INEC

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta ce adadin masu sa ido na cikin gida da na kasashen waje sun kai 146,913, wanda za su sanya ido a babban zabe na ranar 25 ga watan Fabrairu da 11 ga Maris.

Shugaban hukumar INEC, Farfesa Mahmood Yakubu ne ya bayyana haka a ranar Talata a Abuja, a wajen wani taro na masu sa ido kan zaben da aka gudanar a cibiyar tattara bayanai ta kasa da kasa (ICC).

  • Sin Ta Yi Kira Ga Al’ummar Kasa Da Kasa Da Ta Kara Mai Da Hankali Kan Batun Somaliya
  • NNPP Ta Zargi DSS Da Firgita Mambobinta Da Kai Samame Ofisoshinta Na Kano

Farfesa Mahmood ya bayyana cewa, a bisa kyakykyawan tsarin a duniya, hukumomin zabe suna gayyaci kungiyoyi na cikin gida da na kasa da kasa masu sa ido kan harkokin zabe ko kuma shirya rangadin nazari ga manajojin zabe a lokacin zabe, yana mai bayanin cewa rahotanni da shawarwarin masu sa ido suna taimaka wa hukumar zabe wajen samun ci gaba mai dorewa.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “A zaben 2023, wanda za a fara a karshen makon nan na zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisun tarayya, hukumar ta amince da kungiyoyin  masu sa ido na cikin gida 196 wanda suka kasance guda 144,800.

“Hakazalika, hukumar ta amince da kungiyoyin kasa da kasa 33, inda ta suka turo masu sa ido 2,113. A dunkule dukkan kungiyoyi guda 229 ne masu sa ido, wanda suka kasance jimilla 146,913 da za su saka ido a zaben 2023.

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi

An Yi Tir Da ‘Yan Takarar Da Suka Fice Daga APC Saboda Faduwa Zabe

“Wannan shi ne mafi girman yawan masu sa ido na cikin gida da na waje a tarihin zaben Nijeriya.”

Yayin da yake gargadin masu sa ido kan yin katsalandan a zaben, ya ce, “Ku masu saka ido ne kawai. Ka da ku tsoma baki cikin tsari ko nuna bangaranci. Bugu da kari, dole ne masu sa ido na kasa da kasa su kasance masu jagoranci ta hanyar cewa Tarayyar Nijeriya ce ke gudanar da zabukan wanda kuma ya zama dole a mutunta ‘yancin kai.”

Da take jawabi a wurin, Daraktar yankin Afirka na gidauniyar kasa da kasa kan tsarin zabe (IFES), Clara Cole, ta bukaci masu sa ido na kasa da kasa da na cikin gida da su bi dokokin INEC.

A halin da ake ciki, jam’iyyun siyasa 18 suka shiga zaben sun tura wakilan rumfunan zabe miliyan 1.5 da wakilai 68,057 domin gudanar da zabukan na ranar 25 ga Fabrairu da 11 ga Maris.

Wannan yana kunshe ne a cikin rahoton da INEC ta fitar a daren ranar Litinin.

Rahoton ya nuna cewa jam’iyyar PDP ce ke kan gaba da wakilai 176,588, sai jam’iyyar APC da 176,233, sannan jam’iyyar NNPP tana da 176,200, sai kuma jam’iyyar LP da ke da 134,874.

INEC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi
Tsaro

Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi

June 5, 2026
An Yi Tir Da ‘Yan Takarar Da Suka Fice Daga APC Saboda Faduwa Zabe
Labarai

An Yi Tir Da ‘Yan Takarar Da Suka Fice Daga APC Saboda Faduwa Zabe

June 5, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa Da Wasu Ma’aurata A Abuja
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa Da Wasu Ma’aurata A Abuja

June 5, 2026
Next Post
GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi

Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi

June 5, 2026
An Yi Tir Da ‘Yan Takarar Da Suka Fice Daga APC Saboda Faduwa Zabe

An Yi Tir Da ‘Yan Takarar Da Suka Fice Daga APC Saboda Faduwa Zabe

June 5, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa Da Wasu Ma’aurata A Abuja

Ƴansanda Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa Da Wasu Ma’aurata A Abuja

June 5, 2026
Kotu Ta Yi Gwanjon Kaddarorin Sani Sha’aban Bisa Taurin Bashi

Kotu Ta Yi Gwanjon Kaddarorin Sani Sha’aban Bisa Taurin Bashi

June 5, 2026
An Yi Suka Kan Mayar Da Nijeriya Jujin Jibge Kwantaina Da Ake Shigowa Da Su

An Yi Suka Kan Mayar Da Nijeriya Jujin Jibge Kwantaina Da Ake Shigowa Da Su

June 5, 2026
Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho

Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho

June 5, 2026
Sabon Rikicin Manoma Da Makiyaya yayi Ajalin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Sabon Rikicin Manoma Da Makiyaya yayi Ajalin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 5, 2026
Babu Wani Shiri Na Kwaso ‘Yan Nijeriya Daga Falasdin Ko Isra’ila –Gwamnatin Tarayya

Mulkin Tinubu A Shekara 3:Ina Aka Fito? Ina Aka Dosa?

June 5, 2026
Hajji 2026: Mahajjata 1,905 Sun Dawo Nijeriya Daga Saudiyya

Hajji 2026: Mahajjata 1,905 Sun Dawo Nijeriya Daga Saudiyya

June 5, 2026
Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

June 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.