ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutum 146,913 Za Su Sa Ido A Zaben 2023 –INEC

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
INEC

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta ce adadin masu sa ido na cikin gida da na kasashen waje sun kai 146,913, wanda za su sanya ido a babban zabe na ranar 25 ga watan Fabrairu da 11 ga Maris.

Shugaban hukumar INEC, Farfesa Mahmood Yakubu ne ya bayyana haka a ranar Talata a Abuja, a wajen wani taro na masu sa ido kan zaben da aka gudanar a cibiyar tattara bayanai ta kasa da kasa (ICC).

  • Sin Ta Yi Kira Ga Al’ummar Kasa Da Kasa Da Ta Kara Mai Da Hankali Kan Batun Somaliya
  • NNPP Ta Zargi DSS Da Firgita Mambobinta Da Kai Samame Ofisoshinta Na Kano

Farfesa Mahmood ya bayyana cewa, a bisa kyakykyawan tsarin a duniya, hukumomin zabe suna gayyaci kungiyoyi na cikin gida da na kasa da kasa masu sa ido kan harkokin zabe ko kuma shirya rangadin nazari ga manajojin zabe a lokacin zabe, yana mai bayanin cewa rahotanni da shawarwarin masu sa ido suna taimaka wa hukumar zabe wajen samun ci gaba mai dorewa.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “A zaben 2023, wanda za a fara a karshen makon nan na zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisun tarayya, hukumar ta amince da kungiyoyin  masu sa ido na cikin gida 196 wanda suka kasance guda 144,800.

“Hakazalika, hukumar ta amince da kungiyoyin kasa da kasa 33, inda ta suka turo masu sa ido 2,113. A dunkule dukkan kungiyoyi guda 229 ne masu sa ido, wanda suka kasance jimilla 146,913 da za su saka ido a zaben 2023.

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

“Wannan shi ne mafi girman yawan masu sa ido na cikin gida da na waje a tarihin zaben Nijeriya.”

Yayin da yake gargadin masu sa ido kan yin katsalandan a zaben, ya ce, “Ku masu saka ido ne kawai. Ka da ku tsoma baki cikin tsari ko nuna bangaranci. Bugu da kari, dole ne masu sa ido na kasa da kasa su kasance masu jagoranci ta hanyar cewa Tarayyar Nijeriya ce ke gudanar da zabukan wanda kuma ya zama dole a mutunta ‘yancin kai.”

Da take jawabi a wurin, Daraktar yankin Afirka na gidauniyar kasa da kasa kan tsarin zabe (IFES), Clara Cole, ta bukaci masu sa ido na kasa da kasa da na cikin gida da su bi dokokin INEC.

A halin da ake ciki, jam’iyyun siyasa 18 suka shiga zaben sun tura wakilan rumfunan zabe miliyan 1.5 da wakilai 68,057 domin gudanar da zabukan na ranar 25 ga Fabrairu da 11 ga Maris.

Wannan yana kunshe ne a cikin rahoton da INEC ta fitar a daren ranar Litinin.

Rahoton ya nuna cewa jam’iyyar PDP ce ke kan gaba da wakilai 176,588, sai jam’iyyar APC da 176,233, sannan jam’iyyar NNPP tana da 176,200, sai kuma jam’iyyar LP da ke da 134,874.

INEC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027
Labarai

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
Manyan Labarai

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Next Post
GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

LABARAI MASU NASABA

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026
Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.