ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutum 146,913 Za Su Sa Ido A Zaben 2023 –INEC

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
INEC

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta ce adadin masu sa ido na cikin gida da na kasashen waje sun kai 146,913, wanda za su sanya ido a babban zabe na ranar 25 ga watan Fabrairu da 11 ga Maris.

Shugaban hukumar INEC, Farfesa Mahmood Yakubu ne ya bayyana haka a ranar Talata a Abuja, a wajen wani taro na masu sa ido kan zaben da aka gudanar a cibiyar tattara bayanai ta kasa da kasa (ICC).

  • Sin Ta Yi Kira Ga Al’ummar Kasa Da Kasa Da Ta Kara Mai Da Hankali Kan Batun Somaliya
  • NNPP Ta Zargi DSS Da Firgita Mambobinta Da Kai Samame Ofisoshinta Na Kano

Farfesa Mahmood ya bayyana cewa, a bisa kyakykyawan tsarin a duniya, hukumomin zabe suna gayyaci kungiyoyi na cikin gida da na kasa da kasa masu sa ido kan harkokin zabe ko kuma shirya rangadin nazari ga manajojin zabe a lokacin zabe, yana mai bayanin cewa rahotanni da shawarwarin masu sa ido suna taimaka wa hukumar zabe wajen samun ci gaba mai dorewa.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “A zaben 2023, wanda za a fara a karshen makon nan na zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisun tarayya, hukumar ta amince da kungiyoyin  masu sa ido na cikin gida 196 wanda suka kasance guda 144,800.

“Hakazalika, hukumar ta amince da kungiyoyin kasa da kasa 33, inda ta suka turo masu sa ido 2,113. A dunkule dukkan kungiyoyi guda 229 ne masu sa ido, wanda suka kasance jimilla 146,913 da za su saka ido a zaben 2023.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

“Wannan shi ne mafi girman yawan masu sa ido na cikin gida da na waje a tarihin zaben Nijeriya.”

Yayin da yake gargadin masu sa ido kan yin katsalandan a zaben, ya ce, “Ku masu saka ido ne kawai. Ka da ku tsoma baki cikin tsari ko nuna bangaranci. Bugu da kari, dole ne masu sa ido na kasa da kasa su kasance masu jagoranci ta hanyar cewa Tarayyar Nijeriya ce ke gudanar da zabukan wanda kuma ya zama dole a mutunta ‘yancin kai.”

Da take jawabi a wurin, Daraktar yankin Afirka na gidauniyar kasa da kasa kan tsarin zabe (IFES), Clara Cole, ta bukaci masu sa ido na kasa da kasa da na cikin gida da su bi dokokin INEC.

A halin da ake ciki, jam’iyyun siyasa 18 suka shiga zaben sun tura wakilan rumfunan zabe miliyan 1.5 da wakilai 68,057 domin gudanar da zabukan na ranar 25 ga Fabrairu da 11 ga Maris.

Wannan yana kunshe ne a cikin rahoton da INEC ta fitar a daren ranar Litinin.

Rahoton ya nuna cewa jam’iyyar PDP ce ke kan gaba da wakilai 176,588, sai jam’iyyar APC da 176,233, sannan jam’iyyar NNPP tana da 176,200, sai kuma jam’iyyar LP da ke da 134,874.

INEC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara
Tsaro

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026
Manyan Labarai

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano
Labarai

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
Next Post
GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

June 25, 2026
Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

June 25, 2026
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

June 25, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.