ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutum 146,913 Za Su Sa Ido A Zaben 2023 –INEC

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
INEC

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta ce adadin masu sa ido na cikin gida da na kasashen waje sun kai 146,913, wanda za su sanya ido a babban zabe na ranar 25 ga watan Fabrairu da 11 ga Maris.

Shugaban hukumar INEC, Farfesa Mahmood Yakubu ne ya bayyana haka a ranar Talata a Abuja, a wajen wani taro na masu sa ido kan zaben da aka gudanar a cibiyar tattara bayanai ta kasa da kasa (ICC).

  • Sin Ta Yi Kira Ga Al’ummar Kasa Da Kasa Da Ta Kara Mai Da Hankali Kan Batun Somaliya
  • NNPP Ta Zargi DSS Da Firgita Mambobinta Da Kai Samame Ofisoshinta Na Kano

Farfesa Mahmood ya bayyana cewa, a bisa kyakykyawan tsarin a duniya, hukumomin zabe suna gayyaci kungiyoyi na cikin gida da na kasa da kasa masu sa ido kan harkokin zabe ko kuma shirya rangadin nazari ga manajojin zabe a lokacin zabe, yana mai bayanin cewa rahotanni da shawarwarin masu sa ido suna taimaka wa hukumar zabe wajen samun ci gaba mai dorewa.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “A zaben 2023, wanda za a fara a karshen makon nan na zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisun tarayya, hukumar ta amince da kungiyoyin  masu sa ido na cikin gida 196 wanda suka kasance guda 144,800.

“Hakazalika, hukumar ta amince da kungiyoyin kasa da kasa 33, inda ta suka turo masu sa ido 2,113. A dunkule dukkan kungiyoyi guda 229 ne masu sa ido, wanda suka kasance jimilla 146,913 da za su saka ido a zaben 2023.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

“Wannan shi ne mafi girman yawan masu sa ido na cikin gida da na waje a tarihin zaben Nijeriya.”

Yayin da yake gargadin masu sa ido kan yin katsalandan a zaben, ya ce, “Ku masu saka ido ne kawai. Ka da ku tsoma baki cikin tsari ko nuna bangaranci. Bugu da kari, dole ne masu sa ido na kasa da kasa su kasance masu jagoranci ta hanyar cewa Tarayyar Nijeriya ce ke gudanar da zabukan wanda kuma ya zama dole a mutunta ‘yancin kai.”

Da take jawabi a wurin, Daraktar yankin Afirka na gidauniyar kasa da kasa kan tsarin zabe (IFES), Clara Cole, ta bukaci masu sa ido na kasa da kasa da na cikin gida da su bi dokokin INEC.

A halin da ake ciki, jam’iyyun siyasa 18 suka shiga zaben sun tura wakilan rumfunan zabe miliyan 1.5 da wakilai 68,057 domin gudanar da zabukan na ranar 25 ga Fabrairu da 11 ga Maris.

Wannan yana kunshe ne a cikin rahoton da INEC ta fitar a daren ranar Litinin.

Rahoton ya nuna cewa jam’iyyar PDP ce ke kan gaba da wakilai 176,588, sai jam’iyyar APC da 176,233, sannan jam’iyyar NNPP tana da 176,200, sai kuma jam’iyyar LP da ke da 134,874.

INEC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.