A farkon wannan watan, ministan noma ya ƙaddamar da sabon kwamitin gudanarwa na Bankin Noma, inda tsohowar ƴar majalisar wakilai, Kha’amuna Ibrahim Khadi, ta samu muƙamin darakta janar mai kula da haɗari.Khadi ta wakilci mazaɓar Jere na Jihar Borno a tsakanin 2011 zuwa 2015 kuma ita ce kaɗai mace da ta samu nasarar lashe zaɓe a cikin siyasa mai tsauri a jihar.
Khadi, wacce ita ce mataimakiyar shugaban kwamitin sufuri na ruwa a majalisar wakilai, ta ɓace daga harkokin siyasa bayan rashin cin nasara a sake zaɓenta.
Tare da sauran sabbin mambobin da aka ƙaddamar, wanda suka haɗa da Muhammad Babangida a matsayin shugaban kwamitin da Ayodeji Sotinrin a matsayin daraktan gudanarwa, an bai wa Khadi wannan muƙami ta hannun Shugaba Bola Tinubu a Disamba 2025.
Manufar Babban Bankin Noma ita ce tallafa wa ɓangaren noma na Nijeriya ta hanyar samar da rance mai sauƙin samu, goyon bayan ayyuka da za su iya samar da ayyukan yi, samar da abinci, karfafa al’ummomin karkara da kuma ci gaban tattalin arziki mai ɗorewa.














