Majalisar Kula da alƙalai ta amince da ɗaga likkafar sabbin alƙalai 12 zuwa kutun ɗaukaka ƙara tare da dakatar da wasu alƙalai biyu na tsawon shekara guda ba tare da albashi ba saboda zargin saɓa dokokin aiki.
An cimma matsayar ne a taro na 111 na majalisar da aka gudanar ranar 13 ga Mayun 2026 ƙarƙashin jagorancin Babbar Alƙalin Alƙalan Nijeriya, Kudirat Kekere-Ekun.
Majalisar ta ce matakin na da nufin cike guraben da suka biyo bayan ritaya da ƙarin girma a ɓangaren shari’a tare da ƙarfafa aikin kotuna domin inganta gudanar da adalci. Daga cikin waɗanda aka ɗaga zuwa Kotun Ɗaukaka Ƙara akwai James Kolawole Omotosho, da Emeka Nwite, da Sanusi Kado da sauran su.
Haka kuma majalisar ta amince da naɗin Christine T. Clement Ende a matsayin alƙalin babbar kotun jihar Binuwe, yayin da Ibrahim Abdullahi Yakubu da Bala Salisu Daura suka samu amincewa a matsayin alƙalan Kotun Ɗaukaka Ƙarar Shari’ar Musulunci ta jihar Katsina.
A ɓangaren ladabtarwa kuwa, NJC ta dakatar da Ibrahim D. Shekarau da Edward A. E. Okpe na shekara guda ba tare da albashi ba bisa abin da ta kira rashin bin ƙa’ida wajen bayar da umarnin kotu. Haka kuma majalisar ta yi watsi da ƙorafe-ƙorafe 73 da aka shigar kan wasu ma’aikatan shari’a, yayin da ta tura wasu ƙorafe-ƙorafe 11 domin ci gaba da bincike.















Discussion about this post