ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NDLEA Ta Kwace Kwayoyin Pregabalin 75,000 Da Hodar Iblis 556 A Kano

by Rabi'u Ali Indabawa
4 months ago
NDLEA

Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta kasa, NDLEA, reshen Kano, ta kama kwayoyin Pregabalin guda 75,000, kwalaben maganin tari mai dauke da Codeine 556, da kuma wasu adadin tabar wiwi (Cannabis satiba) a yankin Badawa na Kano.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar, Sadik Muhammad-Maigatari, ya fitar a ranar Litinin a Kano.

  • Wang Yi Ya Zanta Ta Wayar Tarho Da Ministar Harkokin Wajen Birtaniya 
  • Aikin Zamantar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya Zai Rage Wa Kasa Asasar Naira Tiriliyan Daya —Dantsoho

Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya, (NAN), ya ruwaito cewa Pregabalin magani ne da ake amfani da shi wajen rage radadi da kuma maganin cutar farfadiya, amma hukumar NDLEA ta ce a cikin ‘yan shekarun nan ya zama daya daga cikin magungunan da ake yawan amfani da su ba bisa ka’ida ba a Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Da yake mayar da martani kan wannan kamen, kwamandan NDLEA a Kano, Dahiru Yahaya-Lawal, ya ce an samu nasarar kwace miyagun kwayoyin ne bayan sahihan bayanan sirri da suka nuna cewa an shirya rarraba su ne a lokacin bukukuwan Eid al-Fitr da ke tafe.

Ya ce, “Wannan samame ya dakile wani babban shiri na rarraba miyagun kwayoyi zuwa kasuwannin haramtattun kwayoyi.”

LABARAI MASU NASABA

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

NDLEA ta kuma bayyana cewa babban wanda ake zargi da hannu a safarar kwayoyin ya tsere, kuma yanzu haka an saka sunansa cikin jerin mutanen da ake nema ruwa a jallo.

“Wannan kamen ya yi wa hanyar sadarwar wannan kungiyar fataucin miyagun kwayoyi babbar illa, kuma ya kare al’ummar Kano daga illolin wadannan kwayoyi,” in ji Yahaya-Lawal.

Ya kara da cewa rundunar za ta ci gaba da bin umarnin shugaban NDLEA kuma babban jami’in gudanarwa na hukumar, Mohamed Buba Marwa, domin tabbatar da an samu al’umma marar miyagun kwayoyi, tare da ci gaba da yaki da sha da fataucin kwayoyi.

Hakazalika, ya yaba wa jama’a bisa ci gaba da ba hukumar hadin kai, tare da rokonsu su rika ba da bayanai masu amfani da za su taimaka wajen dakile safarar miyagun kwayoyi.

Yahaya-Lawal ya kuma gargadi duk masu hannu a harkar safarar miyagun kwayoyi da su daina, yana mai jaddada cewa hukumar ba za ta gajiya ba wajen kamo masu laifi tare da gurfanar da su a gaban doka. (NAN)

NDLEA
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

MASU ALAKA

Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Kotu Da Ɗansanda

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

June 18, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Next Post
Yadda Shigo Da Shinkafa Daga Kasashen Waje Ya Share Masana’antu 90 A Nijeriya

Yadda Shigo Da Shinkafa Daga Kasashen Waje Ya Share Masana’antu 90 A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

July 14, 2026
Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

July 14, 2026
“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

July 14, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

July 14, 2026
Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

July 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.