Tsohon Ministan Sufuri, Rotimi Amaechi, ya yi watsi da sakamakon zaɓen fidda gwani na shugaban ƙasa na jam’iyyar ADC, inda ya bayyana cewa ba a gudanar da shi cikin gaskiya da adalci ba.
Amaechi ya ce an hana yawancin ‘yan jam’iyya a sassa daban-daban na ƙasar nan damar kaɗa ƙuri’a a zaɓen da aka gudanar a ranar Litinin.
Ya kuma zargi jam’iyyar da rashin gaskiya da maguɗi a tsarin zaɓen.
Ya ce ba zai amince da sakamakon kowanne zaɓe ba sai idan an gudanar da shi cikin gaskiya da adalci.
Ɗaya daga cikin ɗan takarar, Mohammed Hayatu-Deen, shi ma ya janye daga zaɓen, yana mai cewa ya lura da rashin daidaito a yayin aikin.
Zaɓen fidda gwani na ADC na ci gaba da gudana a Abuja, kuma shi ne zai tantance wanda zai zama ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar a zaɓen 2027.
Jam’iyyar ADC ta ce ta jajirce wajen tabbatar da dimokuraɗiyya da zaɓe na gaskiya a cikin jam’iyyar.















Discussion about this post