ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NFF Na Duba Yiwuwar Soke Wasan Sada Zumunci Da Kasar Iran

by Abba Ibrahim Wada
3 months ago
NFF

Hukumar kwallon kafa ta Nijeriya ta ce tana sa ido sosai kan rikicin da ke kara tabarbarewa tsakanin kasashen Iran, Amurka da Israila, yayin da rashin tabbas ke karuwa game da shirye-shiryen wasannin sada zumunta na kasa da kasa da tawagar kwallon kafa ta Nijeriya da takwararta ta kasar Iran, in ji wani rahoton da jaridar PUNCH Sports Edtra ta ruwaito.

Tun da farko an shirya Nijeriya za ta shiga gasar hadaka ta kasashe hudu da za a buga a Amman, inda Super Eagles za ta fafata da Iran a ranar 27 ga watan Maris kafin ta hadu da tawagar kwallon kafa ta Jordan mai masaukin baki a ranar 31 ga watan na Maris.

  • Za a Gudanar Da Tattaunawa Kan Batun Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka a Faransa Daga Ranar 14 Zuwa 17 Ga Watan Maris
  • Duniya Ta Shaida Kokarin Sin Bisa Shirin Ci Gaban Tattalin Arziki Da Zamantakewar Al’Umma Na Shekaru Biyar-Biyar Karo Na 15

Hakazalika kuma ana sa ran tawagar kwallon kafa ta Costa Rica na cikin kasashen da za su buga karamar gasar, duk da haka an jefa shakku kan shirin bayan da Iran ta janye daga gasar a daidai lokacin da rikicin siyasa da na soja ke karuwa a Gabas ta Tsakiya, dan jaridar ESPN Colin Udoh ya ruwaito a karshen mako cewa masu shirya gasar suna binciken yiwuwar mayar da wasannin daga Gabas ta Tsakiya zuwa Turai saboda dalilai na tsaro.

ADVERTISEMENT

Da yake magana da PUNCH Sports Edtra, daraktan sadarwa na NFF Ademola Olajire ya ce ana ci gaba da tattaunawa yayin da hukumomi ke ci gaba da sa ido kan lamarin, lokacin da aka tambaye su ko akwai wata kasa ta Turai da ake ganin za a iya mayar da gasar zuwa can, Olajire ya ce alhakin hakan yana kan masu shirya gasar.

Rikicin ya karu ne bayan da Amurka da Isra’ila suka kaddamar da wani hari na hadin gwiwa akan Iran a ranar 28 ga Fabrairu, wanda ya haifar da daukar fansa a duk fadin yankin, kasashe da dama tun daga lokacin sun fuskanci hare-haren makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuka, wanda ya tilasta rufe sararin samaniya da kuma haifar da fargabar tsaro da suka fara shafar ayyukan wasanni.

LABARAI MASU NASABA

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

Sakamakon janyewar Iran, shirin da aka yi na kasashen hudu tun da farko ba shi da tabbas, masu shirya gasar suna tunanin shirya wani wasa na sada zumunci tsakanin Nijeriya da Jordan a wani wuri mai tsaro a nahiyar Turai idan gasar ba za ta ci gaba kamar yadda aka tsara ba.

Shugaban hukumar kwallon kafa ta Nijeriya Ibrahim Gusau ya nuna cewa hukumar har yanzu tana da lokaci domin tantance matakin da za a dauka, buga akalla wasa daya na sada zumunci a lokacin a watan Maris ya kasance babban abin da Super Eagles ke sa ido a kai, yayin da zakarun na gasar cin kofin Afirka sau uku ke ci gaba da kokarin ganin sun farfado ta tawagar.

NFF
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Kasan ‘Yanwasan Da Za Su Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe?
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Ta Samu Lambobin Yabo 16 A Wasannin Tseren Keke
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Za Ta Karbi Bakuncin Babban Taron Hukumar CAF Na Bana
  • Abba Ibrahim Wada
    Shin Ko Arsenal Za Ta Mamaye Duniya?

MASU ALAKA

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya
Wasanni

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa
Wasanni

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

June 2, 2026
Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta
Adabi

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta

May 31, 2026
Next Post
Shawarar GGI Ta Sin Na Ingiza Daidaito Ga Duniya Mai Fama Da Tangal-Tangal

Shawarar GGI Ta Sin Na Ingiza Daidaito Ga Duniya Mai Fama Da Tangal-Tangal

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.