ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NFF Na Duba Yiwuwar Soke Wasan Sada Zumunci Da Kasar Iran

by Abba Ibrahim Wada
6 months ago
NFF

Hukumar kwallon kafa ta Nijeriya ta ce tana sa ido sosai kan rikicin da ke kara tabarbarewa tsakanin kasashen Iran, Amurka da Israila, yayin da rashin tabbas ke karuwa game da shirye-shiryen wasannin sada zumunta na kasa da kasa da tawagar kwallon kafa ta Nijeriya da takwararta ta kasar Iran, in ji wani rahoton da jaridar PUNCH Sports Edtra ta ruwaito.

Tun da farko an shirya Nijeriya za ta shiga gasar hadaka ta kasashe hudu da za a buga a Amman, inda Super Eagles za ta fafata da Iran a ranar 27 ga watan Maris kafin ta hadu da tawagar kwallon kafa ta Jordan mai masaukin baki a ranar 31 ga watan na Maris.

  • Za a Gudanar Da Tattaunawa Kan Batun Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka a Faransa Daga Ranar 14 Zuwa 17 Ga Watan Maris
  • Duniya Ta Shaida Kokarin Sin Bisa Shirin Ci Gaban Tattalin Arziki Da Zamantakewar Al’Umma Na Shekaru Biyar-Biyar Karo Na 15

Hakazalika kuma ana sa ran tawagar kwallon kafa ta Costa Rica na cikin kasashen da za su buga karamar gasar, duk da haka an jefa shakku kan shirin bayan da Iran ta janye daga gasar a daidai lokacin da rikicin siyasa da na soja ke karuwa a Gabas ta Tsakiya, dan jaridar ESPN Colin Udoh ya ruwaito a karshen mako cewa masu shirya gasar suna binciken yiwuwar mayar da wasannin daga Gabas ta Tsakiya zuwa Turai saboda dalilai na tsaro.

ADVERTISEMENT

Da yake magana da PUNCH Sports Edtra, daraktan sadarwa na NFF Ademola Olajire ya ce ana ci gaba da tattaunawa yayin da hukumomi ke ci gaba da sa ido kan lamarin, lokacin da aka tambaye su ko akwai wata kasa ta Turai da ake ganin za a iya mayar da gasar zuwa can, Olajire ya ce alhakin hakan yana kan masu shirya gasar.

Rikicin ya karu ne bayan da Amurka da Isra’ila suka kaddamar da wani hari na hadin gwiwa akan Iran a ranar 28 ga Fabrairu, wanda ya haifar da daukar fansa a duk fadin yankin, kasashe da dama tun daga lokacin sun fuskanci hare-haren makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuka, wanda ya tilasta rufe sararin samaniya da kuma haifar da fargabar tsaro da suka fara shafar ayyukan wasanni.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

Sakamakon janyewar Iran, shirin da aka yi na kasashen hudu tun da farko ba shi da tabbas, masu shirya gasar suna tunanin shirya wani wasa na sada zumunci tsakanin Nijeriya da Jordan a wani wuri mai tsaro a nahiyar Turai idan gasar ba za ta ci gaba kamar yadda aka tsara ba.

Shugaban hukumar kwallon kafa ta Nijeriya Ibrahim Gusau ya nuna cewa hukumar har yanzu tana da lokaci domin tantance matakin da za a dauka, buga akalla wasa daya na sada zumunci a lokacin a watan Maris ya kasance babban abin da Super Eagles ke sa ido a kai, yayin da zakarun na gasar cin kofin Afirka sau uku ke ci gaba da kokarin ganin sun farfado ta tawagar.

NFF
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Yaushe Za A Fara Kofin Zakarun Turai
  • Abba Ibrahim Wada
    Messi Ya Yi Ritaya A Argentina: Da Me Za Mu Iya Tuna Gwarzon Duniyar?
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye ‘Yan wasan Nijeriya Da Za Su Buga Gasar Firimiyar Ingila Ta Bana?
  • Abba Ibrahim Wada
    Chelsea A Ƙarƙashin Xavi Alonso

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana
Wasanni

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

September 8, 2026
Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain
Wasanni

Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain

September 7, 2026
Next Post
Shawarar GGI Ta Sin Na Ingiza Daidaito Ga Duniya Mai Fama Da Tangal-Tangal

Shawarar GGI Ta Sin Na Ingiza Daidaito Ga Duniya Mai Fama Da Tangal-Tangal

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.