Ma’aikatar bunƙasa kiwon dabbobi ta ƙasa, yunƙuro domin daƙile ɓullar wata mummunar cuta da a turance ake kiran ta da ‘Boɓine’ da ke kama shanu a ɗaukacin faɗin ƙasar nan. Ta yunƙuro ɗin ne, ta hanyar ƙaddamar wata tawaga da za ta mayar da hankali, wajen daƙile yaɗuwar cutar zuwa ga shanun da ke ɗaukacin faɗin ƙasar.
Babban ministan ma’aikatar, Idi Mukhtar Maiha, ya sanar da cewa; cutar ta kasance wata babbar annoba, wadda kuma ke ci gaba da shafar fannin bunƙasa kiwon shanu a ƙasashen duniya. A cewarsa, an ƙiyasta cewa; ta harbi shanu aƙalla miyan 54.5 a faɗin wannan ƙasa.
- Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
- Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
- Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
- ’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP
- An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
Kazalika, an gabatar da wasu alƙaluma da ke nuna irin mummunar ɓarnar da ta yi.
A hukumance, aƙalla guda 131 ta ɓarke, inda ta bazu zuwa jihohi 17, inda alƙaluma suka nuna cewa; an samu bazuwar ɓarkewarta ne, sakamakon giɓin da aka samu na rashin sanya ido da kai rahoto ga tsarin gudanar da kiwon shanu a ƙasar.
Cutar dai, na rage ƙimar da ya kamata a samu daga shanu da kuma shafar samar da namansu da madara mai yawa, wadda kuma ke janyo mutuwar shanun da suka kamu da ita.
Maiha ya zayyano wasu daga cikin hanyoyin da ke sanyawa shanun ke kamuwa da cutar da suka haɗa da yadda suke bin hanyoyin da mutane ke wucewa, ƙarancin yi wa shanun allurar rigakafin kare su daga kamuwa da cututtuka da kuma rashin samar da tsarin saurin gano cututtukan da ke harbin shanun.
Ya yi gargaɗin cewa, idan har ba a samar da ɗauki a kan lokaci ba, cutar za ta ci gaba da yaɗuwa, wanda hakan zai haifar wa masu kiwon shanu a ƙasar nan babbar asara
Sabuwar tawagar da aka ƙaddamar, za ta samar da tsarin kare yaɗuwar cutar tare da tabbatar da ganin an samar da shirin yi wa shanu allurar rigakafin kare su daga kamuwa da cututtuka, musamman na zmani.
Ma’aikatar ta kuma buƙaci a yi haɗaka da ɓangaren kiwon shanu masu zaman kansu, musamman don cimma burin daƙile bazuwar cutar a matakin jihohi da kuma na tarayya.
A nata jawabin, babbar sakatariya a ma’aikatar, Chinyere Ijeoma Akujobi ta ce, an samar da wannan ɗaukin ne da nufin saita fannin kiwon dabbobi a ƙasar tare da kuma ƙarfafa wa masu kiwon shanu guiwa a dukkanin faɗin ƙasar.
Wasu daga cikin hukumomin kula da lafiya na ƙasa da ƙasa, kamar hukumar kula da lafiya ta duniya (WHO), sun ayyana bayar da goyon bayansu, inda suka bayar da shawarar ƙarfafa sanya ido kan ɓullar duk wata cuta da ke harbin shanu a Nijeriya.
Sauran masu ruwa da tsaki a fannin kiwo da suka haɗa da Hukumar Abinci da Aikin Noma ta Majalisar Ɗinkin Duniya da Ƙungiyar Fulani Makiyaya ta Ƙasa, wato Miyetti Allah da kuma hukumar kula da Lafiyar Dabbobi ta Duniya, duk sun nuna sha’awarsu ta taimakawa, domin daƙile bazuwar cutar.















Discussion about this post