ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Yunƙuro Don Daƙile Ɓarkewar Sabuwar Cutar Da Ke Kama Shanu

by Abubakar Abba
3 months ago

Ma’aikatar bunƙasa kiwon dabbobi ta ƙasa, yunƙuro domin daƙile ɓullar wata mummunar cuta da a turance ake kiran ta da ‘Boɓine’ da ke kama shanu a ɗaukacin faɗin ƙasar nan. Ta yunƙuro ɗin ne, ta hanyar ƙaddamar wata tawaga da za ta mayar da hankali, wajen daƙile yaɗuwar cutar zuwa ga shanun da ke ɗaukacin faɗin ƙasar.

Babban ministan ma’aikatar, Idi Mukhtar Maiha, ya sanar da cewa; cutar ta kasance wata babbar annoba, wadda kuma ke ci gaba da shafar fannin bunƙasa kiwon shanu a ƙasashen duniya. A cewarsa, an ƙiyasta cewa; ta harbi shanu aƙalla miyan 54.5 a faɗin wannan ƙasa.

  • Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
  • Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Kazalika, an gabatar da wasu alƙaluma da ke nuna irin mummunar ɓarnar da ta yi.

ADVERTISEMENT

A hukumance, aƙalla guda 131 ta ɓarke, inda ta bazu zuwa jihohi 17, inda alƙaluma suka nuna cewa; an samu bazuwar ɓarkewarta ne, sakamakon giɓin da aka samu na rashin sanya ido da kai rahoto ga tsarin gudanar da kiwon shanu a ƙasar.

Cutar dai, na rage ƙimar da ya kamata a samu daga shanu da kuma shafar samar da namansu da madara mai yawa, wadda kuma ke janyo mutuwar shanun da suka kamu da ita.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Maiha ya zayyano wasu daga cikin hanyoyin da ke sanyawa shanun ke kamuwa da cutar da suka haɗa da yadda suke bin hanyoyin da mutane ke wucewa, ƙarancin yi wa shanun allurar rigakafin kare su daga kamuwa da cututtuka da kuma rashin samar da tsarin saurin gano cututtukan da ke harbin shanun.

Ya yi gargaɗin cewa, idan har ba a samar da ɗauki a kan lokaci ba, cutar za ta ci gaba da yaɗuwa, wanda hakan zai haifar wa masu kiwon shanu a ƙasar nan babbar asara

Sabuwar tawagar da aka ƙaddamar, za ta samar da tsarin kare yaɗuwar cutar tare da tabbatar da ganin an samar da shirin yi wa shanu allurar rigakafin kare su daga kamuwa da cututtuka, musamman na zmani.

Ma’aikatar ta kuma buƙaci a yi haɗaka da ɓangaren kiwon shanu masu zaman kansu, musamman don cimma burin daƙile bazuwar cutar a matakin jihohi da kuma na tarayya.

A nata jawabin, babbar sakatariya a ma’aikatar, Chinyere Ijeoma Akujobi ta ce, an samar da wannan ɗaukin ne da nufin saita fannin kiwon dabbobi a ƙasar tare da kuma ƙarfafa wa masu kiwon shanu guiwa a dukkanin faɗin ƙasar.

Wasu daga cikin hukumomin kula da lafiya na ƙasa da ƙasa, kamar hukumar kula da lafiya ta duniya (WHO), sun ayyana bayar da goyon bayansu, inda suka bayar da shawarar ƙarfafa sanya ido kan ɓullar duk wata cuta da ke harbin shanu a Nijeriya.

Sauran masu ruwa da tsaki a fannin kiwo da suka haɗa da Hukumar Abinci da Aikin Noma ta Majalisar Ɗinkin Duniya da Ƙungiyar Fulani Makiyaya ta Ƙasa, wato Miyetti Allah da kuma hukumar kula da Lafiyar Dabbobi ta Duniya, duk sun nuna sha’awarsu ta taimakawa, domin daƙile bazuwar cutar.

Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
Yadda Abubakar Dantsoho Ke Bunƙasa NPA A Tsanake

Yadda Abubakar Dantsoho Ke Bunƙasa NPA A Tsanake

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.