ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Yunƙuro Don Daƙile Ɓarkewar Sabuwar Cutar Da Ke Kama Shanu

by Abubakar Abba
2 months ago

Ma’aikatar bunƙasa kiwon dabbobi ta ƙasa, yunƙuro domin daƙile ɓullar wata mummunar cuta da a turance ake kiran ta da ‘Boɓine’ da ke kama shanu a ɗaukacin faɗin ƙasar nan. Ta yunƙuro ɗin ne, ta hanyar ƙaddamar wata tawaga da za ta mayar da hankali, wajen daƙile yaɗuwar cutar zuwa ga shanun da ke ɗaukacin faɗin ƙasar.

Babban ministan ma’aikatar, Idi Mukhtar Maiha, ya sanar da cewa; cutar ta kasance wata babbar annoba, wadda kuma ke ci gaba da shafar fannin bunƙasa kiwon shanu a ƙasashen duniya. A cewarsa, an ƙiyasta cewa; ta harbi shanu aƙalla miyan 54.5 a faɗin wannan ƙasa.

  • Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • ’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP
  • An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

Kazalika, an gabatar da wasu alƙaluma da ke nuna irin mummunar ɓarnar da ta yi.

ADVERTISEMENT

A hukumance, aƙalla guda 131 ta ɓarke, inda ta bazu zuwa jihohi 17, inda alƙaluma suka nuna cewa; an samu bazuwar ɓarkewarta ne, sakamakon giɓin da aka samu na rashin sanya ido da kai rahoto ga tsarin gudanar da kiwon shanu a ƙasar.

Cutar dai, na rage ƙimar da ya kamata a samu daga shanu da kuma shafar samar da namansu da madara mai yawa, wadda kuma ke janyo mutuwar shanun da suka kamu da ita.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

Maiha ya zayyano wasu daga cikin hanyoyin da ke sanyawa shanun ke kamuwa da cutar da suka haɗa da yadda suke bin hanyoyin da mutane ke wucewa, ƙarancin yi wa shanun allurar rigakafin kare su daga kamuwa da cututtuka da kuma rashin samar da tsarin saurin gano cututtukan da ke harbin shanun.

Ya yi gargaɗin cewa, idan har ba a samar da ɗauki a kan lokaci ba, cutar za ta ci gaba da yaɗuwa, wanda hakan zai haifar wa masu kiwon shanu a ƙasar nan babbar asara

Sabuwar tawagar da aka ƙaddamar, za ta samar da tsarin kare yaɗuwar cutar tare da tabbatar da ganin an samar da shirin yi wa shanu allurar rigakafin kare su daga kamuwa da cututtuka, musamman na zmani.

Ma’aikatar ta kuma buƙaci a yi haɗaka da ɓangaren kiwon shanu masu zaman kansu, musamman don cimma burin daƙile bazuwar cutar a matakin jihohi da kuma na tarayya.

A nata jawabin, babbar sakatariya a ma’aikatar, Chinyere Ijeoma Akujobi ta ce, an samar da wannan ɗaukin ne da nufin saita fannin kiwon dabbobi a ƙasar tare da kuma ƙarfafa wa masu kiwon shanu guiwa a dukkanin faɗin ƙasar.

Wasu daga cikin hukumomin kula da lafiya na ƙasa da ƙasa, kamar hukumar kula da lafiya ta duniya (WHO), sun ayyana bayar da goyon bayansu, inda suka bayar da shawarar ƙarfafa sanya ido kan ɓullar duk wata cuta da ke harbin shanu a Nijeriya.

Sauran masu ruwa da tsaki a fannin kiwo da suka haɗa da Hukumar Abinci da Aikin Noma ta Majalisar Ɗinkin Duniya da Ƙungiyar Fulani Makiyaya ta Ƙasa, wato Miyetti Allah da kuma hukumar kula da Lafiyar Dabbobi ta Duniya, duk sun nuna sha’awarsu ta taimakawa, domin daƙile bazuwar cutar.

Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
Yadda Abubakar Dantsoho Ke Bunƙasa NPA A Tsanake

Yadda Abubakar Dantsoho Ke Bunƙasa NPA A Tsanake

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.