ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Yunƙuro Don Daƙile Ɓarkewar Sabuwar Cutar Da Ke Kama Shanu

by Abubakar Abba
3 months ago

Ma’aikatar bunƙasa kiwon dabbobi ta ƙasa, yunƙuro domin daƙile ɓullar wata mummunar cuta da a turance ake kiran ta da ‘Boɓine’ da ke kama shanu a ɗaukacin faɗin ƙasar nan. Ta yunƙuro ɗin ne, ta hanyar ƙaddamar wata tawaga da za ta mayar da hankali, wajen daƙile yaɗuwar cutar zuwa ga shanun da ke ɗaukacin faɗin ƙasar.

Babban ministan ma’aikatar, Idi Mukhtar Maiha, ya sanar da cewa; cutar ta kasance wata babbar annoba, wadda kuma ke ci gaba da shafar fannin bunƙasa kiwon shanu a ƙasashen duniya. A cewarsa, an ƙiyasta cewa; ta harbi shanu aƙalla miyan 54.5 a faɗin wannan ƙasa.

  • Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa
  • Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kazalika, an gabatar da wasu alƙaluma da ke nuna irin mummunar ɓarnar da ta yi.

ADVERTISEMENT

A hukumance, aƙalla guda 131 ta ɓarke, inda ta bazu zuwa jihohi 17, inda alƙaluma suka nuna cewa; an samu bazuwar ɓarkewarta ne, sakamakon giɓin da aka samu na rashin sanya ido da kai rahoto ga tsarin gudanar da kiwon shanu a ƙasar.

Cutar dai, na rage ƙimar da ya kamata a samu daga shanu da kuma shafar samar da namansu da madara mai yawa, wadda kuma ke janyo mutuwar shanun da suka kamu da ita.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Maiha ya zayyano wasu daga cikin hanyoyin da ke sanyawa shanun ke kamuwa da cutar da suka haɗa da yadda suke bin hanyoyin da mutane ke wucewa, ƙarancin yi wa shanun allurar rigakafin kare su daga kamuwa da cututtuka da kuma rashin samar da tsarin saurin gano cututtukan da ke harbin shanun.

Ya yi gargaɗin cewa, idan har ba a samar da ɗauki a kan lokaci ba, cutar za ta ci gaba da yaɗuwa, wanda hakan zai haifar wa masu kiwon shanu a ƙasar nan babbar asara

Sabuwar tawagar da aka ƙaddamar, za ta samar da tsarin kare yaɗuwar cutar tare da tabbatar da ganin an samar da shirin yi wa shanu allurar rigakafin kare su daga kamuwa da cututtuka, musamman na zmani.

Ma’aikatar ta kuma buƙaci a yi haɗaka da ɓangaren kiwon shanu masu zaman kansu, musamman don cimma burin daƙile bazuwar cutar a matakin jihohi da kuma na tarayya.

A nata jawabin, babbar sakatariya a ma’aikatar, Chinyere Ijeoma Akujobi ta ce, an samar da wannan ɗaukin ne da nufin saita fannin kiwon dabbobi a ƙasar tare da kuma ƙarfafa wa masu kiwon shanu guiwa a dukkanin faɗin ƙasar.

Wasu daga cikin hukumomin kula da lafiya na ƙasa da ƙasa, kamar hukumar kula da lafiya ta duniya (WHO), sun ayyana bayar da goyon bayansu, inda suka bayar da shawarar ƙarfafa sanya ido kan ɓullar duk wata cuta da ke harbin shanu a Nijeriya.

Sauran masu ruwa da tsaki a fannin kiwo da suka haɗa da Hukumar Abinci da Aikin Noma ta Majalisar Ɗinkin Duniya da Ƙungiyar Fulani Makiyaya ta Ƙasa, wato Miyetti Allah da kuma hukumar kula da Lafiyar Dabbobi ta Duniya, duk sun nuna sha’awarsu ta taimakawa, domin daƙile bazuwar cutar.

Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
Yadda Abubakar Dantsoho Ke Bunƙasa NPA A Tsanake

Yadda Abubakar Dantsoho Ke Bunƙasa NPA A Tsanake

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.