ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Na Yunkurin Mayar Wa Da Manoman Tumatir Asarar Da Suka Yi Ta Naira Biliyan 1.3

by Abubakar Abba
3 months ago
Manoman

Gwamnatin tarayya ta yunkuro, wajen samar da shirye-shiyen magance asarar da mamoman Tumatir ke tabkawa a kasar.

Idan za a iya tunawa, a watan Mayun shekarar 2025 ne, Ma’aikatar Aikin Noma da Samar da Wataccen Abinci ta Tarayya, ta kiyasta cewa; cutar ta lalata gonakin da ake noman Tumatir, inda momansa suka yi asarar kimanin naira biliyan 1.3, wanda hakan ya kuma jawo tashin gwaron zabin Tumatirin a dukkanin kasuwannin kasar nan.

  • Yawan Dazuzzuka Da Filin Ciyayi a Kasar Sin Ya Wuce Kashi 56%
  • Kawar Da Dukkanin Haraji Kan Hajojin Da Ake Shigarwa Kasar Sin Daga Afirka Zai Bunkasa Cinikayyar Albarkatun Gona Na Afirka Ta Kudu

Hakan ne ya sa, Ma’aikatar Aikin Noma da Samar da Wataccen Abinci ta Tarayya, ta kaddamar da wani shiri na musamman, don lalubo mafita a kan wannan matsala, domin dakile yaduwar cutar zuwa sauran gonakin da cutar ba ta kai ga yaduwa ba.

ADVERTISEMENT

Misali, wata kwayar halitta da ke cin ganye da kuma sauran kayan lambu, na iya jawo wa manoma asarar da ta kai daga kashi 80 zuwa 100, matukar ba a dauki matakan kare ta da gaggawa ba.

Wanann na zuwa ne dai, bayan samun wasu rahotanni da aka alakanta su da barkewar annobar cutar a shakarar da ta gabata, da ake kira a turance, ‘Tuta absoluta’, wadda ta bulla a wasu gonakin da aka shuka Tutamar, musamman a jihohin Kano, Katsina da kuma Kaduna.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Bugu da kari, bisa wasu alkaluma da hukumar gudanar da bincike a fannin aikin noma ta kasa (NAERLS) ta fitar, sun bayyana cewa, a shekarar 2024 a kasar nan, an noma Tumatir,  din da ya kai kimanin tan miliyan 3.73.

A cewar alkaluman, kimin hekta 824,000 manoman Tumatir a fadin kasar nan suka noma, wanda hakan ya nuna cewa; ba a iya samun wadataccen nomansa a shekarar ta 2024 ba.

Haka zalika, wannan fadakarwar za ta kara taimaka wa da kuma rabar da kayan aikin noman Tumatirin da suka kamata, musamman domin samar da daukin da ya kamata na dakile yaduwar wannana cuta da ke lalata gonakin da ake nomansu.

Kaza lika, a karkashin wani shirin noma na nau’ikan Tumatir da ake kira a turance ‘HORTITOM4’ da kuma ‘HORTITOM5’, wasu masu bincike ne a fannin nomansa suka kirkiro da su a shekarar 2025.

Mahukuntan, sun gudanar da yin gwaje-gwajen ne na  wannan shiri a wasu gonakin, na yin noman na Tumatir da kuma a gonakin da ake yin nomansa da rani.

Wasu jami’ai a bangaren na noman nasa, sun bayyana cewa; wadannan nau’ikan na shirin noman Tumatirin, wato ‘HORTITOM4 da HORTITOM5’, sun kasance suna bijire wa dukkannin wani nau’i na cuta da za ta iya lalata shi, bayan an shuka Irin na Tumatirin.

Bugu da kari, manomi zai kuma iya samun yin girbin Tumatirin da zai kai daga kimanin tan 21.7 zuwa tan 27.2 daga cikin kowacce hekta daya da ya shuka Irin na Tumatirin.

“A kasar nan dai, Tumatir ba wai kadai ana nomansa tare kuma da yin amfani da shi ba ne, wata hanya ce da ke kara samar da kudaden shiga ga wadanda suka rungumi yin noman nasa, musamman a tsakanin kananan manoman da ke fadin wannan kasa.

Kasar nan dai, ta kasance tana daya daga cikin manyan kasashen da ke a nahiyar Afirka, wajen nomansa da kuma samar da shi mai dimbin yawan gaske.

Kazalika, a kwanakin baya, an ruwaito karamin Minista na Ma’aikatar Aikin Noma da Samar da Wataccen Abinci ta Tarayya, Dakta Aliyu Sabi Abdullahi ya bayyana cewa; fannin na kuma kara samar da ayyukanyi da yin jigilarsa zuwa kasuwanni, domin sayar da shi da kuma sarrafa shi zuwa wasu nau’ika daban-daban.

Bugu da kari, Hukumar Kula da Bincike Kan Harkokin Noma da Ayyukan Malaman Gona ta Kasa, wato NAERLS a cikin wani rahotan da ta fitar, ta sake bayyana sake bullar cutar ta Tuta absoluta  a shekarar 2024, musamman a Jihar Kano.

Manoman
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
Sin Na Adawa Da Lalata Tsarin Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Duniya Bisa Kafa “Karamin Rukuni”

Sin Na Adawa Da Lalata Tsarin Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Duniya Bisa Kafa “Karamin Rukuni”

LABARAI MASU NASABA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.