ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Na Yunkurin Mayar Wa Da Manoman Tumatir Asarar Da Suka Yi Ta Naira Biliyan 1.3

by Abubakar Abba
6 months ago
Manoman

Gwamnatin tarayya ta yunkuro, wajen samar da shirye-shiyen magance asarar da mamoman Tumatir ke tabkawa a kasar.

Idan za a iya tunawa, a watan Mayun shekarar 2025 ne, Ma’aikatar Aikin Noma da Samar da Wataccen Abinci ta Tarayya, ta kiyasta cewa; cutar ta lalata gonakin da ake noman Tumatir, inda momansa suka yi asarar kimanin naira biliyan 1.3, wanda hakan ya kuma jawo tashin gwaron zabin Tumatirin a dukkanin kasuwannin kasar nan.

  • Yawan Dazuzzuka Da Filin Ciyayi a Kasar Sin Ya Wuce Kashi 56%
  • Kawar Da Dukkanin Haraji Kan Hajojin Da Ake Shigarwa Kasar Sin Daga Afirka Zai Bunkasa Cinikayyar Albarkatun Gona Na Afirka Ta Kudu

Hakan ne ya sa, Ma’aikatar Aikin Noma da Samar da Wataccen Abinci ta Tarayya, ta kaddamar da wani shiri na musamman, don lalubo mafita a kan wannan matsala, domin dakile yaduwar cutar zuwa sauran gonakin da cutar ba ta kai ga yaduwa ba.

ADVERTISEMENT

Misali, wata kwayar halitta da ke cin ganye da kuma sauran kayan lambu, na iya jawo wa manoma asarar da ta kai daga kashi 80 zuwa 100, matukar ba a dauki matakan kare ta da gaggawa ba.

Wanann na zuwa ne dai, bayan samun wasu rahotanni da aka alakanta su da barkewar annobar cutar a shakarar da ta gabata, da ake kira a turance, ‘Tuta absoluta’, wadda ta bulla a wasu gonakin da aka shuka Tutamar, musamman a jihohin Kano, Katsina da kuma Kaduna.

LABARAI MASU NASABA

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Bugu da kari, bisa wasu alkaluma da hukumar gudanar da bincike a fannin aikin noma ta kasa (NAERLS) ta fitar, sun bayyana cewa, a shekarar 2024 a kasar nan, an noma Tumatir,  din da ya kai kimanin tan miliyan 3.73.

A cewar alkaluman, kimin hekta 824,000 manoman Tumatir a fadin kasar nan suka noma, wanda hakan ya nuna cewa; ba a iya samun wadataccen nomansa a shekarar ta 2024 ba.

Haka zalika, wannan fadakarwar za ta kara taimaka wa da kuma rabar da kayan aikin noman Tumatirin da suka kamata, musamman domin samar da daukin da ya kamata na dakile yaduwar wannana cuta da ke lalata gonakin da ake nomansu.

Kaza lika, a karkashin wani shirin noma na nau’ikan Tumatir da ake kira a turance ‘HORTITOM4’ da kuma ‘HORTITOM5’, wasu masu bincike ne a fannin nomansa suka kirkiro da su a shekarar 2025.

Mahukuntan, sun gudanar da yin gwaje-gwajen ne na  wannan shiri a wasu gonakin, na yin noman na Tumatir da kuma a gonakin da ake yin nomansa da rani.

Wasu jami’ai a bangaren na noman nasa, sun bayyana cewa; wadannan nau’ikan na shirin noman Tumatirin, wato ‘HORTITOM4 da HORTITOM5’, sun kasance suna bijire wa dukkannin wani nau’i na cuta da za ta iya lalata shi, bayan an shuka Irin na Tumatirin.

Bugu da kari, manomi zai kuma iya samun yin girbin Tumatirin da zai kai daga kimanin tan 21.7 zuwa tan 27.2 daga cikin kowacce hekta daya da ya shuka Irin na Tumatirin.

“A kasar nan dai, Tumatir ba wai kadai ana nomansa tare kuma da yin amfani da shi ba ne, wata hanya ce da ke kara samar da kudaden shiga ga wadanda suka rungumi yin noman nasa, musamman a tsakanin kananan manoman da ke fadin wannan kasa.

Kasar nan dai, ta kasance tana daya daga cikin manyan kasashen da ke a nahiyar Afirka, wajen nomansa da kuma samar da shi mai dimbin yawan gaske.

Kazalika, a kwanakin baya, an ruwaito karamin Minista na Ma’aikatar Aikin Noma da Samar da Wataccen Abinci ta Tarayya, Dakta Aliyu Sabi Abdullahi ya bayyana cewa; fannin na kuma kara samar da ayyukanyi da yin jigilarsa zuwa kasuwanni, domin sayar da shi da kuma sarrafa shi zuwa wasu nau’ika daban-daban.

Bugu da kari, Hukumar Kula da Bincike Kan Harkokin Noma da Ayyukan Malaman Gona ta Kasa, wato NAERLS a cikin wani rahotan da ta fitar, ta sake bayyana sake bullar cutar ta Tuta absoluta  a shekarar 2024, musamman a Jihar Kano.

Manoman
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

MASU ALAKA

Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka
Noma Da Kiwo

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

August 1, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
Noma Da Kiwo

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Next Post
Sin Na Adawa Da Lalata Tsarin Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Duniya Bisa Kafa “Karamin Rukuni”

Sin Na Adawa Da Lalata Tsarin Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Duniya Bisa Kafa “Karamin Rukuni”

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.