ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Na Yunkurin Mayar Wa Da Manoman Tumatir Asarar Da Suka Yi Ta Naira Biliyan 1.3

by Abubakar Abba
4 months ago
Manoman

Gwamnatin tarayya ta yunkuro, wajen samar da shirye-shiyen magance asarar da mamoman Tumatir ke tabkawa a kasar.

Idan za a iya tunawa, a watan Mayun shekarar 2025 ne, Ma’aikatar Aikin Noma da Samar da Wataccen Abinci ta Tarayya, ta kiyasta cewa; cutar ta lalata gonakin da ake noman Tumatir, inda momansa suka yi asarar kimanin naira biliyan 1.3, wanda hakan ya kuma jawo tashin gwaron zabin Tumatirin a dukkanin kasuwannin kasar nan.

  • Yawan Dazuzzuka Da Filin Ciyayi a Kasar Sin Ya Wuce Kashi 56%
  • Kawar Da Dukkanin Haraji Kan Hajojin Da Ake Shigarwa Kasar Sin Daga Afirka Zai Bunkasa Cinikayyar Albarkatun Gona Na Afirka Ta Kudu

Hakan ne ya sa, Ma’aikatar Aikin Noma da Samar da Wataccen Abinci ta Tarayya, ta kaddamar da wani shiri na musamman, don lalubo mafita a kan wannan matsala, domin dakile yaduwar cutar zuwa sauran gonakin da cutar ba ta kai ga yaduwa ba.

ADVERTISEMENT

Misali, wata kwayar halitta da ke cin ganye da kuma sauran kayan lambu, na iya jawo wa manoma asarar da ta kai daga kashi 80 zuwa 100, matukar ba a dauki matakan kare ta da gaggawa ba.

Wanann na zuwa ne dai, bayan samun wasu rahotanni da aka alakanta su da barkewar annobar cutar a shakarar da ta gabata, da ake kira a turance, ‘Tuta absoluta’, wadda ta bulla a wasu gonakin da aka shuka Tutamar, musamman a jihohin Kano, Katsina da kuma Kaduna.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Bugu da kari, bisa wasu alkaluma da hukumar gudanar da bincike a fannin aikin noma ta kasa (NAERLS) ta fitar, sun bayyana cewa, a shekarar 2024 a kasar nan, an noma Tumatir,  din da ya kai kimanin tan miliyan 3.73.

A cewar alkaluman, kimin hekta 824,000 manoman Tumatir a fadin kasar nan suka noma, wanda hakan ya nuna cewa; ba a iya samun wadataccen nomansa a shekarar ta 2024 ba.

Haka zalika, wannan fadakarwar za ta kara taimaka wa da kuma rabar da kayan aikin noman Tumatirin da suka kamata, musamman domin samar da daukin da ya kamata na dakile yaduwar wannana cuta da ke lalata gonakin da ake nomansu.

Kaza lika, a karkashin wani shirin noma na nau’ikan Tumatir da ake kira a turance ‘HORTITOM4’ da kuma ‘HORTITOM5’, wasu masu bincike ne a fannin nomansa suka kirkiro da su a shekarar 2025.

Mahukuntan, sun gudanar da yin gwaje-gwajen ne na  wannan shiri a wasu gonakin, na yin noman na Tumatir da kuma a gonakin da ake yin nomansa da rani.

Wasu jami’ai a bangaren na noman nasa, sun bayyana cewa; wadannan nau’ikan na shirin noman Tumatirin, wato ‘HORTITOM4 da HORTITOM5’, sun kasance suna bijire wa dukkannin wani nau’i na cuta da za ta iya lalata shi, bayan an shuka Irin na Tumatirin.

Bugu da kari, manomi zai kuma iya samun yin girbin Tumatirin da zai kai daga kimanin tan 21.7 zuwa tan 27.2 daga cikin kowacce hekta daya da ya shuka Irin na Tumatirin.

“A kasar nan dai, Tumatir ba wai kadai ana nomansa tare kuma da yin amfani da shi ba ne, wata hanya ce da ke kara samar da kudaden shiga ga wadanda suka rungumi yin noman nasa, musamman a tsakanin kananan manoman da ke fadin wannan kasa.

Kasar nan dai, ta kasance tana daya daga cikin manyan kasashen da ke a nahiyar Afirka, wajen nomansa da kuma samar da shi mai dimbin yawan gaske.

Kazalika, a kwanakin baya, an ruwaito karamin Minista na Ma’aikatar Aikin Noma da Samar da Wataccen Abinci ta Tarayya, Dakta Aliyu Sabi Abdullahi ya bayyana cewa; fannin na kuma kara samar da ayyukanyi da yin jigilarsa zuwa kasuwanni, domin sayar da shi da kuma sarrafa shi zuwa wasu nau’ika daban-daban.

Bugu da kari, Hukumar Kula da Bincike Kan Harkokin Noma da Ayyukan Malaman Gona ta Kasa, wato NAERLS a cikin wani rahotan da ta fitar, ta sake bayyana sake bullar cutar ta Tuta absoluta  a shekarar 2024, musamman a Jihar Kano.

Manoman
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
Sin Na Adawa Da Lalata Tsarin Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Duniya Bisa Kafa “Karamin Rukuni”

Sin Na Adawa Da Lalata Tsarin Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Duniya Bisa Kafa “Karamin Rukuni”

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.