ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NNPC Da Matatar Dangote Na Gasar Rage Farashin Fetur

by Khalid Idris Doya
1 year ago
NNPC

A wani abun da ake kallo a matsayin maida martani ga rage farashin farko da matatar Mai ta Dangote ta yi, kamfanin kula da albarkatun mai ta kasa (NNPCL), ya rage farashin litar mai daga naira 945 zuwa naira 860 a Legas da kuma naira 865 a Abuja. 

Tuni gidajen man NNPC a sassa daban-daban musamman a Ori-Oke, Egbe, Ikoyi, da na kan hanyar Ikorodu a Legas suka sauya sabon farashi, yayin da haka zancen yake a gidajen man NNPC a Abuja da suka hada da Lugbe da Ketampe.

  • Nazarin CGTN: Manufar Sanya Muradun Amurka Gaba Da Komai Na Lalata Dangantakar Dake Tsakaninta Da Turai
  • Ƴar Majalisar Dattawa Natasha Akpoti Na Fuskantar Dakatarwar Wata Shida

Su ma gidajen mai masu zaman kansu da suke karkashin kungiyar dillalan mai ta IPMAN sun ce tuni mambobinsu suka rage farashin litar mai duk kuwa da cewa man da suke da su a halin yanzu sun saye su ne a kan tsohon farashi mai da tsada, domin su ci gaba da kasancewa cikin gasar cinikin mai.

ADVERTISEMENT

Ko da yake kamfanin NNPCL dai bai fito a hukumance ya fadi dalilin rage farashin litar mai din ba, amma ana ganin kamar hakan ya biyo bayan yadda ‘yan Nijeriya ke zaben gidajen mai masu sauki domin sayen mai da kuma halin matsin da jama’a kasa ke fuskanta.

Wani kwararren masani kan makamashi, Wunmi Iledare, ya soki matatar Dangote da NNPCL kan kokuwar rage farashin, yana mai cewa ba ragewa ba matsalar dorewar saukin farashin shi ne abun da jama’an kasa ke da bukata a halin yanzu.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

“NNPC na amfani da kayayyakin da ake shigowa da su daga kasashen waje domin yin gogayya da matatar Dangote, a maimakon ta dukufa amfani da matatunta na mai da suke cikin kasar nan. Wannan lamarin na shafan dorewar musayar kasuwanci kuma zai kara janyo damuwowi ne kawai ga tattalin arzikin kasar nan,” Iledare ya shaida.

Wani masanin makamashi kuma shugaban NES, Farfesa Adeola Adenikinju, ya ce akwai bukatar hukumomi su dauki matakan da suka dace domin tabbatar da wadatar mai da kuma saukinsa a kasuwanni.

Ya kuma lura da cewa akwai bukatar magance dakile gasar rashin adalci domin a samu yin ciniki sosai a tsakanin masu mai.

Mataimakin shugaban IPMAN, Hammed Fashola, ya nuna farin ciki da rage farashin litar mai, wanda ya yi nuni da cewa mafi yawan ‘yan Nijeriya da ita suka dogara.

Ya tabbatar da cewa dillalan mai da dama sun fara sayar da mai a gidajen mansu kan farashin mai rahusan duk kuwa da cewa sun sayi mai din a farashi mai tsada.

Fashola ya ce, “Yayin da NNPCL ke sayar da mai kan lita guda a naira 860 a gidajen manta, amma sabon farashin bai nuna haka ba, amma ana ta kokarin sabuntawa.”

Duk kokarin jin ta bakin mai magana da yawun NNPC, Femi Soneye, ya citura.

NNPC
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi
Labarai

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Next Post
Matakin Amurka Na Kakaba Haraji Kan Kayayyakin Sin Ta Fakewa Da Batun Sinadarin Fentanyl Bai Dace Ba

Matakin Amurka Na Kakaba Haraji Kan Kayayyakin Sin Ta Fakewa Da Batun Sinadarin Fentanyl Bai Dace Ba

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.