Jam’iyyar NNPP ta yi watsi da hukuncin kotun sauraren zaben gwamnan Kano, ta ce wannan abin dariya ne a ce an tsige dan takararta, gwamna Abba Yusuf, wanda nasararsa ta fito fili.
A cikin wata sanarwa da shugaban Jam’iyyar na kasa, Kawu Ali, ya fitar, ya ce NNPP ta samu bata yarda da yadda kotun ta yanke hukuncin a shari’ar zaben gwamnan Kano ba, inda ta kira hukuncin da rashin adalci.
- DA DUMI-DUMI: Kotu Ta Kori Gwamna Abba Gida-Gida Ta Tabbatar Da Nasarar Gawuna
- An Sanya Dokar Hana Fita Ta Tsawon Sa’o’i 24 A Jihar Kano
Jam’iyyar NNPP ta ce, za ta daukaka kara kan hukuncin kotun, kazalika shugaban ya yi kira ga mambobin kungiyar da magoya bayansu da su kwantar da hankalinsu yana mai cewa hukuncin ba zai tsaya anan ba.
A wata tattaunawa ta wayar tarho da Odita na kasa kuma mukaddashin sakataren yada labarai na kasa, Oladipo Johnson, ya ce jam’iyyar har yanzu ba ta karanta hukuncin ba kuma kotu ba ta da dalilin tsige gwamnan nasu.