ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NPA Ta Kaddamar Da Tsarin Kara Bunkasa Fitar Da Kayan Da Basu Da Nasaba Da Fannin Mai

by Bello Hamza and Sulaiman
3 months ago
NPA

Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Kasa ta kasa ta kaddamar da cikakken tsari, domin ta kara habaka fannin da bai shafi fitar da man fetur ba.

Hakan na kunshe ne, a cikin sanawar da jaridar Punch ta samu daga gun NPA, a ranar Lahadin da ta gabata.

  • CBN Ya Ɗage Tsarin Dijital, Zai Biya Mahajjata Kuɗin Guzurinsu A Hannu
  • INEC Ta Gyara Jadawalin Zaben 2027 Tare Da Tsawaita Wa’adin Mika Rajistar Jam’iyyun Siyasa

A cewar sanarwar Shugaban hukumar Dakta Abubakar Dantsoho, ne ya bayyana haka a taro karo na 37 da cibiyar baje koli ta kasuwanci, masana’antu, ma’adanai da kuma aikin noma ta jihar Enugu ta shirya.

ADVERTISEMENT

Ya ce, NPA na kan kara saita tsarin tafiyar da fannin na sufurin jiragen ruwan kasa, domin a hada masu sarrafa kaya na cikin gida, musamman, domin amfanin kanana da kuma matsakaitan sana’aoi, domin su kai mataki, irin na duniya.

Dantsoho ya zayyano irin mahimmancin da jihar ta Enugu, take da shi, a bangaren hada-hadar kasuwanci, musamman a tsakanin Kudu Maso Gabashin kasa

LABARAI MASU NASABA

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya

Ya kara da cewa, yadda tsarin jihar yake, ya kasance akwai dimbin damar da za a iya amfana da ita, wajen fitar da kayan da aka sarrafaa, a cikin kasar, zuwa ketare, musamman kayan da suka sahfi amfanin gona.

Ya kuma yabwa cibiyar, musamman ci gaban da take ci gaba da samarwa wajen bunkasa kasuwanci da kuma gudanar da hada-hadar kasuwanci, ta kasa da kasa.

Ya ci gaba da cewa, a bisa kokarin da ake yi na rage cunkoso a tashoshin jiragen ruwan kasa da kuma kara inganta ayyukan NPA, D antsoho ya bayyana cewa, NPA na kan zuba jari, na gudanar da aikin yin garanbawul a tashoshin jiragen ruwa na Onne, Warri, da kuma na Calabar.

A cewarsa, NPA na kuma ci gaba da taimaka wa, sabbin tashoshin jiragen ruwa na yankuna.

“Gangane da sabunta zuba jari da muka zuba a kan kayan aiki a tashoshin da ke a yankin Gabas, mun samar da ka’ida, na irin kayan da za a yi aiki da su a tashoshin jiragen ruwa, musamman domin a magance, duk wani cunkoson jiragen ruwa, a tashoshin,” Inji Dantsoho.

Ya sanar da cewa, fannin hada-hadar kasuwanci, ya kasance daya daga cikin ginshikan da ke kara habaka tatalin arzikin kasar nan.

Ya kara da cewa, NPA ta himmatu wajen ganin ta kawar da duk wani tsaiko da ke kawo cikasa, wajen fitar da kayan da aka sarrafa, a cikin kasar, musamman domin a kara bayar da damar gudanar da gasa, a bangaren hada-hadar kasuwanci.

A cewarsa, sauye-sauyen da NPA ta kirkiro da su a bangaren fitar da kaya zuwa ketare, an kirkiro da su ne, domin samar da saukin fitar da kayan da aka sarrafa a kasar

“Kamar yadda wasu ke da masaniya kan tsarin da NPA ta kirikiro da shi na EPT, na ci gaba da taimaka wa wajen fitar da kaya zuwa ketare,” A cewar Dantsoho.

Shugaban ya kara da cewa, domin a kara inganta sahihancin ayyukan hukumar da kuma samar da saukin yin kasuwanci, wadanda suka yi daidai da tsarin kasuwanci na gwamnatin tarayya NPA, na ci gaba da wanzar da tsarin NSW na kasa.

“Domin a samun cin yawan dogaro kan ayyukan ‘yan Adam, hukumar ta kara mayar da hankali, wajen yin amfani da tsarin na NSW,” Inji shugaban.

Ya sanar da cewa, a yanzu wannan tsarin na NSW, shi ne ake yin amfani da shi, a fadin duniya, tare da kuma hada masu ruwa da tsaki damar gudanar da hada-hadar kasuwancinsu.

Dantsoho ya kuma bai wa masu ruwan da tsaki da masu zuba jari da kuma masu fitar da kaya zuwa kasar waje, tabbacin cewa, hukumar a shirye take domin ta yi hadaka da su.

Ya kuma yi kira a gare su, da su yi amfani da damar da hukumar ta NPA ta samar domin su kara bunkasa ayyukansu.

”Kofar mu ako da yaushe, a bude take domin yin hadaka, mun kuma samar da matakai domin cimma burin da hukumar, ta sanya a gaba, “ Inji Dantsoho.

NPA
Bello Hamza
+ posts Bio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar Kansilolin APC Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Idan Ba A Daina Zargin Sanata Yari Ba
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya
NPA
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin
  • Sulaiman
    Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya
  • Sulaiman
    Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara
  • Sulaiman
    Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

MASU ALAKA

NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN
Tattalin Arziki

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

June 27, 2026
Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani
Tattalin Arziki

Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya

June 26, 2026
Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
Tattalin Arziki

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

June 20, 2026
Next Post
Kano Pillars Sun Yi Alƙawarin Sake Zage Damtse Bayan Rashin Nasarar Wasan Bayelsa

Kano Pillars Sun Yi Alƙawarin Sake Zage Damtse Bayan Rashin Nasarar Wasan Bayelsa

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

July 7, 2026
Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

July 7, 2026
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

ADC Ta Zargi Gwamnatin Tinubu Da Jefa ‘Yan Nijeriya Miliyan 17 Cikin Yunwa

July 7, 2026
Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

July 6, 2026
Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026
Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

July 6, 2026
FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

July 6, 2026
Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

Shugabannin Sin Da Montenegro Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

July 7, 2026
Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

July 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.