ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NPA Ta Kaddamar Da Tsarin Kara Bunkasa Fitar Da Kayan Da Basu Da Nasaba Da Fannin Mai

by Bello Hamza and Sulaiman
2 months ago
NPA

Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Kasa ta kasa ta kaddamar da cikakken tsari, domin ta kara habaka fannin da bai shafi fitar da man fetur ba.

Hakan na kunshe ne, a cikin sanawar da jaridar Punch ta samu daga gun NPA, a ranar Lahadin da ta gabata.

  • CBN Ya Ɗage Tsarin Dijital, Zai Biya Mahajjata Kuɗin Guzurinsu A Hannu
  • INEC Ta Gyara Jadawalin Zaben 2027 Tare Da Tsawaita Wa’adin Mika Rajistar Jam’iyyun Siyasa

A cewar sanarwar Shugaban hukumar Dakta Abubakar Dantsoho, ne ya bayyana haka a taro karo na 37 da cibiyar baje koli ta kasuwanci, masana’antu, ma’adanai da kuma aikin noma ta jihar Enugu ta shirya.

ADVERTISEMENT

Ya ce, NPA na kan kara saita tsarin tafiyar da fannin na sufurin jiragen ruwan kasa, domin a hada masu sarrafa kaya na cikin gida, musamman, domin amfanin kanana da kuma matsakaitan sana’aoi, domin su kai mataki, irin na duniya.

Dantsoho ya zayyano irin mahimmancin da jihar ta Enugu, take da shi, a bangaren hada-hadar kasuwanci, musamman a tsakanin Kudu Maso Gabashin kasa

LABARAI MASU NASABA

Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe

Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho

Ya kara da cewa, yadda tsarin jihar yake, ya kasance akwai dimbin damar da za a iya amfana da ita, wajen fitar da kayan da aka sarrafaa, a cikin kasar, zuwa ketare, musamman kayan da suka sahfi amfanin gona.

Ya kuma yabwa cibiyar, musamman ci gaban da take ci gaba da samarwa wajen bunkasa kasuwanci da kuma gudanar da hada-hadar kasuwanci, ta kasa da kasa.

Ya ci gaba da cewa, a bisa kokarin da ake yi na rage cunkoso a tashoshin jiragen ruwan kasa da kuma kara inganta ayyukan NPA, D antsoho ya bayyana cewa, NPA na kan zuba jari, na gudanar da aikin yin garanbawul a tashoshin jiragen ruwa na Onne, Warri, da kuma na Calabar.

A cewarsa, NPA na kuma ci gaba da taimaka wa, sabbin tashoshin jiragen ruwa na yankuna.

“Gangane da sabunta zuba jari da muka zuba a kan kayan aiki a tashoshin da ke a yankin Gabas, mun samar da ka’ida, na irin kayan da za a yi aiki da su a tashoshin jiragen ruwa, musamman domin a magance, duk wani cunkoson jiragen ruwa, a tashoshin,” Inji Dantsoho.

Ya sanar da cewa, fannin hada-hadar kasuwanci, ya kasance daya daga cikin ginshikan da ke kara habaka tatalin arzikin kasar nan.

Ya kara da cewa, NPA ta himmatu wajen ganin ta kawar da duk wani tsaiko da ke kawo cikasa, wajen fitar da kayan da aka sarrafa, a cikin kasar, musamman domin a kara bayar da damar gudanar da gasa, a bangaren hada-hadar kasuwanci.

A cewarsa, sauye-sauyen da NPA ta kirkiro da su a bangaren fitar da kaya zuwa ketare, an kirkiro da su ne, domin samar da saukin fitar da kayan da aka sarrafa a kasar

“Kamar yadda wasu ke da masaniya kan tsarin da NPA ta kirikiro da shi na EPT, na ci gaba da taimaka wa wajen fitar da kaya zuwa ketare,” A cewar Dantsoho.

Shugaban ya kara da cewa, domin a kara inganta sahihancin ayyukan hukumar da kuma samar da saukin yin kasuwanci, wadanda suka yi daidai da tsarin kasuwanci na gwamnatin tarayya NPA, na ci gaba da wanzar da tsarin NSW na kasa.

“Domin a samun cin yawan dogaro kan ayyukan ‘yan Adam, hukumar ta kara mayar da hankali, wajen yin amfani da tsarin na NSW,” Inji shugaban.

Ya sanar da cewa, a yanzu wannan tsarin na NSW, shi ne ake yin amfani da shi, a fadin duniya, tare da kuma hada masu ruwa da tsaki damar gudanar da hada-hadar kasuwancinsu.

Dantsoho ya kuma bai wa masu ruwan da tsaki da masu zuba jari da kuma masu fitar da kaya zuwa kasar waje, tabbacin cewa, hukumar a shirye take domin ta yi hadaka da su.

Ya kuma yi kira a gare su, da su yi amfani da damar da hukumar ta NPA ta samar domin su kara bunkasa ayyukansu.

”Kofar mu ako da yaushe, a bude take domin yin hadaka, mun kuma samar da matakai domin cimma burin da hukumar, ta sanya a gaba, “ Inji Dantsoho.

NPA
Bello Hamza
+ posts Bio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Yadda Oyetola Ya Ƙaddamar Da Babban Taron Ƙungiyar  PMAWCA A Legas
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Lokaci Ya Yi Da Matasan Nijeriya Za Su Ƙwato Ƙasarsu — Kwamred Yahaya Abdullahi
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kamfanin Dangote Na Kara Karfafa Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Jihar Neja
NPA
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

MASU ALAKA

Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
Tattalin Arziki

Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe

May 29, 2026
Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho
Tattalin Arziki

Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho

May 29, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Tattalin Arziki

Yadda Oyetola Ya Ƙaddamar Da Babban Taron Ƙungiyar  PMAWCA A Legas

May 24, 2026
Next Post
Kano Pillars Sun Yi Alƙawarin Sake Zage Damtse Bayan Rashin Nasarar Wasan Bayelsa

Kano Pillars Sun Yi Alƙawarin Sake Zage Damtse Bayan Rashin Nasarar Wasan Bayelsa

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.