ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Philippines Ba Ta Da Imani Ko Kadan

by CGTN Hausa
2 years ago
Philippines

LABARAI MASU NASABA

Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

Ministan tsaron kasar Philippines, Gilberto Teodoro ya bayyana a shekaranjiya 27 ga wata cewa, tun da gwamnatin kasar mai ci ta hau karagar mulki a shekara ta 2022, kawo yanzu, ma’aikatar tsaron kasar ba ta da masaniya, kana, ba ta taba cimma wata yarjejeniya da kasar Sin, game da rikicinsu kan tekun kudancin kasar Sin ba. Wannan ya shaida cewa, Philippines ta sake musunta yarjejeniyar da ta cimma da kasar Sin kan batun karamin tsibirin Ren’ai Jiao, baya ga musuntawar da shugaban kasar, Ferdinand Marcos, da mashawarcinsa kan harkokin tsaron kasa, Eduardo Ano suka yi.

Domin tabbatar da halin karko da ake ciki a tekun kudancin kasar Sin, kasashen Sin da Philippines sun rattaba hannu kan wata yarjejeniya dangane da batun karamin tsibirin Ren’ai Jiao, a yayin mulkin gwamnatin Rodrigo Duterte. Bisa yarjejeniyar, Philippines ta alkawarta cewa, ba za ta ci gaba da kaiwa jiragen ruwan sojan da ta jibge a can kayayyakin gine-gine ba. Sai dai kuma bisa ra’ayin nuna jin-kai, kasar Sin ta amince da matakin Philippines na kaiwa sojojin jiragen ruwan kayan rayuwa na wani gajeren lokaci. Tun da gwamnati mai ci ta hau karagar mulki a watan Yunin shekara ta 2022 har zuwa watan Fabrairun shekara ta 2023, hukumomin kasashen Sin da Philippines sun kiyaye wannan yarjejeniya, kaza lika, kasar Sin ta gabatar da bayanai sau da dama da suka shafi yarjejeniyar ga manyan jami’an Philippines.

  • Adadin Sabbin Kamfanonin Kimiyya Da Fasaha Masu Saurin Ci Gaba A Kasar Sin Ya Kai 369
  • Li Qiang Ya Jaddada Muhimmancin Gina Tsarin Samar Da Ababen Hawa Masu Aiki Da Sabbin Makamashi Hade Da Na’urori Masu Basira

Amma manyan jami’an Philippines na gwamnati mai ci sun ce ba su da masaniya ko kadan game da yarjejeniyar da gwamnatin da ta shude ta cimma da kasar Sin, sun sani amma sun take sani. Dalilin gwamnatin Philippines na cin amana gami da kaiwa jiragen ruwan sojan da ta jibge ba bisa doka ba kayayyakin gine-gine shi ne, tana yunkurin samun tallafin kasar Amurka, da neman inganta karfin sojanta na ruwa, da cimma burin mamaye karamin tsibirin Ren’ai Jiao har abada. A don haka, har ta zama wata kafa da Amurka take amfani da ita wajen yin shisshigi cikin harkokin shiyyar.

ADVERTISEMENT

Wasu matakan da Amurka ta dauka, na tsallake jan layi, da girke makamai masu linzami masu cin matsakaicin zango a Philippines, za su kara ta’azzara halin da ake ciki a yankin. Hakikanin gaskiya, wadannan abubuwan da Philippines ta yi, tamkar kai kanta ne ga hallaka. Kaza lika, musunta yarjejeniyar da ta yi, zai sa kasar ta zama mai aikata laifi, dake musunta tarihi, da cin amana, gami da haifar da rudani ga halin da ake ciki a shiyyar. (Murtala Zhang)

Philippines
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

MASU ALAKA

Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

June 14, 2026
An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28
Daga Birnin Sin

An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

June 14, 2026
Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin
Daga Birnin Sin

Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin

June 14, 2026
Next Post
Yadda Kasar Sin Ke Samar Da Gudummawa Ga Tabbatar Da Bunkasuwar Duniya Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

Yadda Kasar Sin Ke Samar Da Gudummawa Ga Tabbatar Da Bunkasuwar Duniya Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

LABARAI MASU NASABA

An Daure Ɗan Gidan Gimbiyar Masarautar Norway Shekara 4 Kan Laifin Fyaɗe

An Daure Ɗan Gidan Gimbiyar Masarautar Norway Shekara 4 Kan Laifin Fyaɗe

June 15, 2026
An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

June 15, 2026
Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

June 15, 2026
Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya

Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya

June 14, 2026
Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

June 14, 2026
Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

June 14, 2026
Atiku Ya Soki Shirin Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Bangaren Wutar Lantarki

Atiku Ya Soki Shirin Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Bangaren Wutar Lantarki

June 14, 2026
An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

June 14, 2026
Ododo Ya Kai Ziyara Sansanin Horar Dakarun Tsaro Daji A Kogi

Ododo Ya Kai Ziyara Sansanin Horar Dakarun Tsaro Daji A Kogi

June 14, 2026
Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin

Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin

June 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.