Jam’iyyar PRP ta fito fili ta zargi tsohon gwamnan jihar Kano, injiniya Rabiu Musa Kwankwaso, da laifin sayen fom-fom na takara na jam’iyyar ta hanyar amfani da wasu mutane. Jam’iyyar ta bayyana cewa wannan wata dabarar siyasa ce tsararriya da gangan domin hana tabbatattu da wanɗanda suka cancanta ƴan jam’iyyar damar tsayawa takara a zaɓuka masu zuwa.
A cewar jam’iyyar, Kwankwaso da muƙarrabansa suna ƙoƙarin yin amfani da ƙarfin kuɗi wajen mamaye tsarin PRP ta hanyar saye gurbi da kuma sanya mutanen da ba su da kishin jam’iyyar a matsayin ‘yan takara. Wannan mataki, in ji su, babbar barazana ce ga tsarin dimokuraɗiyya na gaskiya wanda jam’iyyar ta daɗe tana fafutuka a kansa domin kare hakkin talakawa.
Haka kuma, PRP ta jaddada cewa ba za ta lamunci katsalandan ko ƙoƙarin juya akalar jam’iyyar daga waje ba, musamman daga mutanen da ke da wasu manufofi na daban na ƙashin kansu. Sun bayyana cewa an riga an gano maƙarƙashiyar da ake ƙullawa, saboda haka uwar jam’iyya tana ɗaukar ƙwararan matakai na doka domin daƙile dukkan fom-fom din da aka saya ta haramtacciyar hanya.
Jam’iyyar ta kuma yi kira na musamman ga ɗaukacin magoya bayanta da mambobi da su kasance masu sanya ido da kuma kwantar da hankulansu. Ta tabbatar musu da cewa ba za a taɓa barin wasu ‘yan siyasa su ɓata gurbin takara na jam’iyyar ba, kuma za a tabbatar da cewa mutanen da suka cancanta ne kawai suka samu tikitin tsayawa takara ƙarƙashin inuwar PRP.













Discussion about this post