Aƙalla mutane 279 ne aka yi garkuwa da su faɗin Nijeriya a iya watan Mayu na shekarar 2026, yayin da 842 suka rasa rayukansu sakamakon tashe-tashen hakula 156 da aka samu kamar yadda rahoton Nextier’s Nigeria ya bayyana.
Rahotan ya ce an samu aƙalla ƙarin yawan tashe-tashen hankula da suke da alaƙa da rashin tsaro da kusan kashi 51.1 idan aka yi la’akari da watannin baya, yayin da garkuwa da mutane shi ma ya ƙaru da kashi 19.7. Jami’an hukumar da suke kula da bincike da samar da dokoki kuma wanda suka kasance Malamai a Jami’ar Nnamdi Azikiwe da ke Awka ne suka ba5yyana hakan a wata takarda da suka fitar.
Rohotan wada suka yi wa take da Matsalar Tsaron Nijeriya, Matakinta da Kuma Yadda Yadda Ya Yi Ƙamari, ta waiwayi sha’anin Tsaro a watannin baya musamman ma na farkon shekara da kuma matakin tsaron da ake ciki a yanzu.
Rahotan kuma ya yi duba kan hanyoyi da dabaru da Gwamnati da dai-daiku ya kamata su ɗauka dangane da sha’anin tsaro a Nijeriya.













