ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rage Kashe Kudaden Tafiyar Da Gwamnati: Mu Gani A Kasa – ‘Yan Nijeriya

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
gwamnati

‘Yan Nijeriya da dama sun yaba wa Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu kan matakin da ya dauka na rage yawan ’yan rakiyarsa a tafiye-tafiyensa na cikin gida da na kasashen waje, sai dai wasu suna tababa da wannan yunkuri na shugaban kasa domin kuwa an sha jin sanarwa masu kama da wannan amma ba a iya aiwatar da su.

Idan za a iya tunawa, Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya ba da sanarwar zaftare kashi 60 cikin 100 na adadin mukarraban da za su rika yi masa rakiya na tafiye-tafiye da kuma mataimakinsa da sauran jami’an gwamnati.
Wannan dai na zuwa ne a yayin da shugaban kasar ya sanar da rage yawan jami’an da za su rika yi masa rakiya a duk tafiye-tafiyen aiki da zai je a ciki da wajen kasar.

  • Tinubu Ya Bada Umarnin Binciken Ma’aikatar Jin Kai Kan Zargin Karkatar Da Miliyan N585
  • Tinubu Ya Yi Alkawarin Garambawul A Bangaren Lantarki

Matakin ya kuma shafi dukkan ministoci da manyan jami’an gwamnatinsa ciki har da mataimakin shugaban kasa da uwargidan shugaban kasa, wadanda su ma ya ba da umarnin rage adadin jami’an da za su rika yi musu rakiya, kamar yadda Ajuri Ngelale, mashawarci na musamman ga shugaban Nijeriya kan harkar yada labarai ya fitar a cikin wata sanarwa.

ADVERTISEMENT

A cewar Ngelale, matakin wani yunkuri ne na rage yawan kudaden da jami’an gwamnati ke kashewa kan harkokin tafiye-tafiye.

Sanarwar ta ce yawan jami’an da za su rika yi wa shugaban kasar rakiya zuwa kasashen waje, nan gaba ba za su wuce jami’ai 20 ba, yayin da ’yan rakiyarsa a tafiyar cikin gida ba za su wuce jami’ai 25 ba. Sannan kuma sanarwar na cewa Shugaba Tinubu ya ba da umarnin a daina tura dimbin jami’an tsaro zuwa wata jiha a duk lokacin da zai kai ziyara can, maimakon haka za a rika amfani da jami’an tsaron da ke jihar ne kawai don tabbatar da tsaro.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Wannan mataki na zuwa ne makonni biyar bayan da ‘yan Nijeriya suka soki gwamnatin Tinubu na daukan wakilai 1,114 zuwa taron Majalisar Dinkin Duniya a Dubai, duk da yake fadar shugaban kasa ta ce wakilai 422 kawai ta dauka, rahoton dai ya ce an kashe naira bilyan 2.78 a kudin jirgi.

Wasu ‘yan Nijeriya sun bayyana ra’ayoyinsu mabambanta kan wannan lamari.
Tsohon gwamnan Jihar Kano, Malam Ibrahim Shekarau ya bayyana cewa ‘yan Nijeriya sun zuba ido su gani ko za a yi aiki da matakin kar ya zama na fatar baki kawai.

Ya ba da shawarar a kafa wani sashe na musamman a ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya, wanda zai rika sa ido tare da tabbatar da cewa sauran shugabannin ma’aikatu da hukumomin gwamnati sun yi aiki da sabon matakin na shugaban kasa.

Abubakar Sabo ya ce, “Wannan abun a yaba ne, amma sai an aiwatar sannan nan zan nuna godiyata”
Tukur Abdu Zaria, cewa ya yi “Mu gani a kasa wai ana biki a gidan su kare”
Rukayya Shehu ta ce “Da za a aiwatar da wannan kuduri da mun ji dadi”Bashir Dalhatu ya ce “Allah dai ya sa a yi amfani da kudaden wajen inganta ilimi da samar da tsaro da samar da ayyukan yi ga matasa don kuwa shi ne babban matsalar kasar nan”.

gwamnati
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
pate

Farfesa Pate Ya Ja Kunnen ‘Yan Jarida Bisa Rahotannin Karya

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.