ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rage Kashe Kudaden Tafiyar Da Gwamnati: Mu Gani A Kasa – ‘Yan Nijeriya

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
gwamnati

‘Yan Nijeriya da dama sun yaba wa Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu kan matakin da ya dauka na rage yawan ’yan rakiyarsa a tafiye-tafiyensa na cikin gida da na kasashen waje, sai dai wasu suna tababa da wannan yunkuri na shugaban kasa domin kuwa an sha jin sanarwa masu kama da wannan amma ba a iya aiwatar da su.

Idan za a iya tunawa, Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya ba da sanarwar zaftare kashi 60 cikin 100 na adadin mukarraban da za su rika yi masa rakiya na tafiye-tafiye da kuma mataimakinsa da sauran jami’an gwamnati.
Wannan dai na zuwa ne a yayin da shugaban kasar ya sanar da rage yawan jami’an da za su rika yi masa rakiya a duk tafiye-tafiyen aiki da zai je a ciki da wajen kasar.

  • Tinubu Ya Bada Umarnin Binciken Ma’aikatar Jin Kai Kan Zargin Karkatar Da Miliyan N585
  • Tinubu Ya Yi Alkawarin Garambawul A Bangaren Lantarki

Matakin ya kuma shafi dukkan ministoci da manyan jami’an gwamnatinsa ciki har da mataimakin shugaban kasa da uwargidan shugaban kasa, wadanda su ma ya ba da umarnin rage adadin jami’an da za su rika yi musu rakiya, kamar yadda Ajuri Ngelale, mashawarci na musamman ga shugaban Nijeriya kan harkar yada labarai ya fitar a cikin wata sanarwa.

ADVERTISEMENT

A cewar Ngelale, matakin wani yunkuri ne na rage yawan kudaden da jami’an gwamnati ke kashewa kan harkokin tafiye-tafiye.

Sanarwar ta ce yawan jami’an da za su rika yi wa shugaban kasar rakiya zuwa kasashen waje, nan gaba ba za su wuce jami’ai 20 ba, yayin da ’yan rakiyarsa a tafiyar cikin gida ba za su wuce jami’ai 25 ba. Sannan kuma sanarwar na cewa Shugaba Tinubu ya ba da umarnin a daina tura dimbin jami’an tsaro zuwa wata jiha a duk lokacin da zai kai ziyara can, maimakon haka za a rika amfani da jami’an tsaron da ke jihar ne kawai don tabbatar da tsaro.

LABARAI MASU NASABA

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

Wannan mataki na zuwa ne makonni biyar bayan da ‘yan Nijeriya suka soki gwamnatin Tinubu na daukan wakilai 1,114 zuwa taron Majalisar Dinkin Duniya a Dubai, duk da yake fadar shugaban kasa ta ce wakilai 422 kawai ta dauka, rahoton dai ya ce an kashe naira bilyan 2.78 a kudin jirgi.

Wasu ‘yan Nijeriya sun bayyana ra’ayoyinsu mabambanta kan wannan lamari.
Tsohon gwamnan Jihar Kano, Malam Ibrahim Shekarau ya bayyana cewa ‘yan Nijeriya sun zuba ido su gani ko za a yi aiki da matakin kar ya zama na fatar baki kawai.

Ya ba da shawarar a kafa wani sashe na musamman a ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya, wanda zai rika sa ido tare da tabbatar da cewa sauran shugabannin ma’aikatu da hukumomin gwamnati sun yi aiki da sabon matakin na shugaban kasa.

Abubakar Sabo ya ce, “Wannan abun a yaba ne, amma sai an aiwatar sannan nan zan nuna godiyata”
Tukur Abdu Zaria, cewa ya yi “Mu gani a kasa wai ana biki a gidan su kare”
Rukayya Shehu ta ce “Da za a aiwatar da wannan kuduri da mun ji dadi”Bashir Dalhatu ya ce “Allah dai ya sa a yi amfani da kudaden wajen inganta ilimi da samar da tsaro da samar da ayyukan yi ga matasa don kuwa shi ne babban matsalar kasar nan”.

gwamnati
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Next Post
pate

Farfesa Pate Ya Ja Kunnen ‘Yan Jarida Bisa Rahotannin Karya

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.