Tsohon Gwamnan Jihar Edo, Adams Oshiomhole, ya ce rikicin da ke tsakanin manyan ’yan adawa gabanin zaɓen 2027 na taimaka wa jam’iyyar APC mai mulki.
Ya bayyana hakan ne a shirin Politics Today na gidan talabijin na Channels, inda ya ce shugabannin adawa suna caccakar juna maimakon haɗa kai domin ƙalubalantar Shugaba Bola Ahmed Tinubu.
Ya ce tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar na taimaka wa APC ne ba da gangan ba, ta hanyar sukar Peter Obi.
Ya kuma ce Obi ya caccaki tsohon Ministan Sufuri Rotimi Amaechi, yayin da Amaechi shi ma ya kira Obi da Atiku ’yan siyasar yanki ɗaya.
Oshiomhole ya ce ’yan adawa ba su da haɗin kai ko cikakken shiri da zai iya kalubalantar gwamnati.
Ya kuma yi tambaya ko ’yan adawa za su iya janye wasu manyan manufofin Tinubu kamar cire tallafin mai, gyaran haraji da tsarin bai wa ɗaliba bashi.
A cewarsa, tsohon Gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, shi ma na daga cikin manyan ’yan siyasar da za su taka rawa gabanin 2027.















Discussion about this post