Aƙalla maniyyata 664 daga cikin mutum 2,035 da suka yi rajista daga jihar Katsina suka isa ƙasar Saudiyya domin gudanar da aikin Hajjin 2026 ta filin jirgin sama na Umaru Musa Yar’adua.
Rukunin farko na maniyyata 411, waɗanda suka haɗa da maza 283 da mata 128, sun tashi zuwa Madina ranar Litinin cikin jirgin Max Air, yayin da jirgi na biyu da ya ɗauki maniyyata 253 ya tashi ranar Laraba.
Da yake jawabi ga maniyyatan kafin tashinsu, mataimakin gwamnan jihar Katsina, Faruq Lawal-Jobe, ya yi musu addu’ar tafiya lafiya da dawowa gida cikin nasara bayan kammala ibadar Hajji. Ya kuma buƙace su da su kasance jakadu nagari na jihar tare da bin duk dokoki da ka’idojin da aka sanar da su yayin horaswar aikin Hajji.
Shi ma shugaban Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta jihar, Kabir Bature, ya bayyana gamsuwarsa da yadda aka gudanar da tashin rukuni na farko cikin lumana da tsari.
Bature ya ƙara da cewa ana sa ran jirgi na uku zai tashi da tsakar dare domin ɗaukar fiye da maniyyata 400 zuwa Saudiyya, yana mai cewa shirye-shiryen bana sun fi sauƙi saboda matakan farko da gwamnatin jihar da hukumar suka ɗauka tun da wuri.















Discussion about this post