ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin ADC: Lauya Ya Caccaki Kotun Ɗaukaka Ƙara

by Abubakar Sulaiman
2 months ago
ADC

Wani lauya mai zaman kansa a birnin Legas, Liborous Oshoma, ya yi tsokaci mai zurfi kan rikicin shugabanci da ke addabar jam’iyyar ADC, inda ya bayyana cewa hukuncin da Kotun Ɗaukaka Ƙara ta yanke ya ƙara rikita al’amura maimakon warware su, musamman dangane da umarnin da ta bayar na a ci gaba da bin tsarin “status quo ante bellum” duk da cewa ta kori ƙarar da aka shigar a gabanta.

Oshoma, a cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Facebook, ya bayyana cewa tushen rikicin ya samo asali ne daga ƙarar da Nafiu Bala Gombe ya shigar a Babbar Kotun Tarayya, inda yake neman a fassara kundin tsarin mulkin jam’iyyar ADC domin tabbatar da iƙirarinsa na shugabanci bayan murabus ɗin tsohon shugaban jam’iyyar, lamarin da ya haifar da cece-kuce tsakanin ɓangarori daban-daban na jam’iyyar.

  • Komawar Kwankwaso ADC, Zai Jawo Hankalin Manyan ‘Yan Siyasa Zuwa Jam’iyyar 
  • Kano Pillars Sun Yi Alƙawarin Sake Zage Damtse Bayan Rashin Nasarar Wasan Bayelsa

Ya ƙara da cewa, bayan kotun farko ta ƙi amincewa da bukatar bayar da umarnin gaggawa (ex parte), sai ta bukaci a sanar da sauran ɓangarori su zo su kare kansu, amma wannan mataki bai yi wa Sanata David Mark daɗi ba, wanda ya garzaya Kotun Ɗaukaka Ƙara domin ƙalubalantar matakin, sai dai kotun ta ƙi sauraron ƙarar bisa rashin samun izini (leave) daga kotu kamar yadda doka ta tanada.

ADVERTISEMENT

Sai dai duk da korar ƙarar, Oshoma ya nuna damuwa kan yadda Kotun Ɗaukaka Ƙara ta sake bayar da umarni ga ɓangarorin da su ci gaba da bin tsarin da ake ciki, yana mai cewa wannan mataki na iya haifar da rikice-rikicen fassara da kuma ruɗani a tsakanin masu ruwa da tsaki, maimakon samar da mafita mai ɗorewa ga rikicin da ke addabar jam’iyyar.

A cewarsa, mafi dacewa shi ne kotun ta umurci ɓangarorin da su nemi a hanzarta sauraron babbar shari’ar a Babbar Kotun Tarayya, musamman duba da muhimmancin lokaci yayin da ake tunkarar zaɓen 2027, yana mai jaddada cewa jinkiri a irin wannan lamari na iya kawo tangarda ga tsarin dimokuraɗiyya da kuma shirye-shiryen zaɓe a ƙasar.

LABARAI MASU NASABA

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

ADC
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2, Sun Yi Garkuwa Da 30 A Kogi
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Masallaci, Sun Kashe Wani Yaro A Kaduna
  • Abubakar Sulaiman
    Babachir Lawal Ya Fice Daga ADC, Ya Zargi Atiku Da Murɗe Zaben Fidda Gwani

MASU ALAKA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Next Post
Manufar Sin Ta Yafe Harajin Kwastam Ga Afirka: Alfanun Abin Ya Zarce Batun Cinikayya

Manufar Sin Ta Yafe Harajin Kwastam Ga Afirka: Alfanun Abin Ya Zarce Batun Cinikayya

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.