ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Cikin Gida Na Jam’iyyun Siyasa Na Yin Mummunan Tasiri Ga Sahihancin Zaben Nijeriya – INEC

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
5 months ago
INEC

Shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), Farfesa Joash Amupitan ya ce rikici na cikin gida na jam’iyyun siyasa na shafar ingancin zaben Nijeriya.

A yayin da yake magana a taron tuntuba tsakanin hukumar da shugabannin jam’iyyun siyasa da aka yi wa rajista, shugaban INEC ya ce rikice-rikicen shugabanci da ake yawan samu a cikin jam’iyyun siyasa daban-daban a fadin kasar nan yana dawo da hannun agogo baya kan harkokin zabe.

  • Manoma Da Makiyaya Sun Kulla Yarjejeniyar Zaman Lafiya A Filato
  • Karfafa Tsarin Kimiyyar Fintech A Nijeriya

Ya ce shari’u da dama wanda INEC ke yawan samu suna karkatar da hankalin hukumar daga muhimman aikin tabbatar da sahihin zabe mai cike da adalci a Nijeriya. Yana kara da cewa “a matsayinmu na masu samar da tsarin zabe, mun tilasta wa kanmu magance wadannan al’amurra ba don amfanin hukumarmu kawai ba, sai dai don amfanin dimokuradiyyarmu.

ADVERTISEMENT

“Dole ne mu hada kai tare don kare gaskiya cikin harkokin zabenmu, wanda ke fuskantar kalubale daga yawaitar rikicin shugabanci a cikin jam’iyyu daban-daban a fadin kasarmu mai daraja.

“Asalin dimokuradiyya yana cikin ikon jam’iyyun siyasa su bunkasa, yin muhawara, da fafata manufofi ta hanyar da ke girmama ka’idojin na adalci da mutunta juna.

LABARAI MASU NASABA

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

“A ko da yaushe, ina matukar damuwa idan na kalli yadda rikice-rikice ke faruwa a tsakanin shugabannin jam’iyyumu, wanda ba kawai yana rage ma’anar manyan manufofin wadannan kungiyoyin siyasa ba, har ma yana yin tasiri a tsarin bangaren shari’armu da kuma albarkatun kasarmu.

“Wadannan shari’u masu yawa wanda hukumar ta samu kanta a ciki suna karkatar da hankalinmu daga muhimman aikinmu na asali na tabbatar da sahihin zabe mai cike da gaskiya da zai samu amicewar ‘yan Nijeriya. A matsayinmu na masu kula da tsarin zabe, mun tilasta wa kanmu fuskanci wadannan matsaloli ba wai don amfanin hukumar kawai ba, don ci gaban dimokuradiyyarmu.

“Tasirin wadannan rikice-rikice yana da fadi sosai. Suna haifar da yanayi na rashin tabbas ga ‘yan jam’iyya da masu goyon bayansu, suna rage amincewar jama’a ga tsarin siyasa, kuma suna raunana tsarin dimokuradiyya da muke raino. Kowace kara ba wai kawai tana cin lokaci da dukiya ba, har ma tana karkatar da hankalinmu daga muhimmin aikinmu da hankalin masu jefa kuri’a da kuma muhimman batutuwan kasa.”

“A matsayin hukuma mai zaman kanta, INEC ta kasancewa mara son zuciya, amma muna so mu tunatar da dukkan jam’iyyun siyasa cewa jagoranci mai hadin kai da gaskiya yana da muhimmanci ga lafiyar dimokuradiyyarmu. Muna kira ga shugabannin jam’iyya da su bai wa tattaunawa mai amfani fifiko fiye da rigingimu masu raba kawuna, su karfafa hadin kai a cikin jam’iyyunsu, kuma su mayar da hankali kan kirkirar manufofin da za su bunkasa kasa da al’umma maimakon rikicin cikin gida.”

A yayin da yake magana kan rajistar sabbin jam’iyyun siyasa, shugaban INEC ya sanar da rajistar sabbin jam’iyyun siyasa biyu don kawo yawan jam’iyyun a kasar zuwa 21.

Ya tabbatar da cewa hukumar tana nan daram a kan kokarinta na gudanar da harkokin zaben kasa, wanda za ta fara da zaben kananan hukumomin Abuja a ranar 21 ga Fabrairu, 2026, har zuwa zaben gwamnonin na jihohin Ekiti da Osun.

Ya ce, “INEC a karkashin shugabancina zan ci gaba da aiki bisa ga tanadin tsarin dokar zabe da suka hada da kundin tsarin mulkin tarayyar Nijeriya da dokar zabe da ka’idodi da tsare-tsarenmu da kuma umarnin shari’a daga kotuna.

“Yayin da muke kara fuskantar karatowar zaben 2027, yana da matukar muhimmanci mu kasance masu lura da kuma daukar mataki tun kafin lokaci. Dole ne mu shirya don gabatar da tsarin zabe mai inganci wanda ya kunshi ka’idodin dimokuradiyya, adalci, da hadin kai.”

Shugaban cibiyar hadakar jam’iyyu (IPAC), Dakta Yusuf Dantalle, ya ce nauyin da ke gabanmu yana da girma sosai. Abin da ‘yan Nijeriya ke tsammani na samun kasa mai dimbin arziki, karfi, da ci gaba a tsarin dimokuradiyya yana da matukar girma. A matsayinta ta mai kula da zabe, INEC na da babban nauyi na kundin tsarin mulki ya dora mata.

Shugaban IPAC ya ce dole hukumar zabe ta kasance mai ‘yanci, mai adalci, gaskiya, karfi, da tsayuwa wajen gudanar da sahihin zabe wanda ya kasance mai cike da adalci, kuma dole ne koyaushe ta samar da yanayi mai kyau ga dukkan jam’iyyun siyasa da ‘yan takara, tare da lura cewa sahihancinta tana gwada shi duk lokacin da ‘yan kasa suka je zabe.

Ya ce IPAC na sane da rikice-rikicen shugabanci a wasu jam’iyyun siyasa kuma ya bukaci INEC ta bi ka’idojin jam’iyyun wajen magance irin wadannan al’amura, musamman dangane da shugabancin da ta shiga tsakani kuma ta wallafa a shafinta na internet.

INEC
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
INEC
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar
  • Sulaiman
    Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu
  • Sulaiman
    Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026
  • Sulaiman
    Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

MASU ALAKA

makarfi
Tambarin Dimokuradiyya

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
Tambarin Dimokuradiyya

An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

June 26, 2026
Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
Next Post
Sin Ta Nuna Karfinta Na Sarrafa Bayanai Bisa Amfani Da Fasahar AI A Sararin Samaniya

Sin Ta Nuna Karfinta Na Sarrafa Bayanai Bisa Amfani Da Fasahar AI A Sararin Samaniya

LABARAI MASU NASABA

Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

July 4, 2026
Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

July 4, 2026
CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

July 4, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

July 4, 2026
Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

July 4, 2026
Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

July 4, 2026
Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

July 4, 2026
Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026
Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

July 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.