Manoma da makiyaya a cikin kauyuka shida na kananan hukumomin Bokkos da Riyom sun sanya hannu kan yarjejeniyoyi 25 na zaman lafiya don dawo da sulhu da kwanciyar hankali tsakanin mambobin kungiyoyin.
Manoma da makiyayan, ciki har da maza da mata, sun fito ne daga kauyukan Sha, Bum, da Sopp a Bokkos da Riyom, inda mutane da yawa suka rasa rayukansu, kuma dukiya ta lalace a sakamakon rikice-rikice daban-daban.
- Fubara Ya Rushe Majalisar Zartarwa Ta Jihar Ribas
- An Shirya Bikin Share Fagen Shirin Talibijin Na CMG Na Murnar Sabuwar Shekarar Gargajiyar Kasar Sin A Kasashen Rasha da Faransa Da Brasil Da Kuma Koriya Ta Kudu
Sanya hannu kan yarjejeniyoyin ya biyo bayan jerin tattaunawa da Cibiyar Ci gaban Hada Kai (IFIT) ta gudanar don gina hadin kai a cikin al’ummomin karkara masu rauni da rikici, da nufin nemo hanyoyin warware tashin hankali da ya addabi yankunan a baya.
Lazaros Dabid, wani mahalarta taron kuma babban shugaban gunduma a Karamar Hukumar Bokkos, ya bayyana cewa tsarin zaman lafiya yana da matukar muhimmanci ganin kalubalen da suka fuskanta.
Ya bayyana cewa, “Masu shirya taron sun yi nasarar hada al’ummomi, musamman a matakin kasa. Sun bi shirin lokaci bayan lokaci don tabbatar da nasararsa. Sun gano matsalolinmu kuma sun tattauna su tare da mu.
Muna da yakinin cewa za a aiwatar da yarjejeniyoyin. A cikin coci-coci da masallatai, inda kake ganin mutanenka, za mu tabbatar da cewa wannan zaman lafiya ya dawwama.”
Wani mahalarcin taron, Chiroma Haruna Idris, ya ce tsarin zaman lafiya zai taimaka sosai wajen dawo da kwanciyar hankali tsakanin membobin al’ummomin makiyaya da manoma.
Ya ce, “Zuwanmu nan ya taimaka mana fahimtar kalubalen da muke fuskanta, kuma muna da yakinin cewa abin da muka koya zai taimaka mana wajen magance damuwarmu tare cikin lumana ba tare da wata matsala ko rikicewa ba. Yarjejeniyoyin da aka sanya hannu za su taimaka wajen warware matsalolin da suka rage.”















Discussion about this post