ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sabon Shirin Sabunta Fata Shi Ne Ƙashin Bayan Ci Gaban Kasa – Gwamna Gombe

by Leadership Hausa
6 months ago
gombe

Khalid Idris Doya

Gwamnan Jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya, ya bayyana shirin Sabunta Fata na Shugaba Bola Ahmed Tinubu a matsayin salon gwamnatocin da APC ke jagoranta a dukkan matakai don aiwatar da ayyukansu ga ‘yan Nijeriya.

Gwamnan ya yi wannan jawabin ne yayin da ya karbi bakuncin Ko-odinetan Shirin Sabunta Fata na Yankin Arewa Maso Gabas kuma tsohon Gwamnan Jihar Bauchi, Malam Isa Yuguda, a fadar Gwamnati da ke Gombe.

  • Buƙatar A Sake Duba Sabuwar Dokar Haraji
  • Shari’ar Annabi SAW Ta Fi Ta Sauran Annabawa Sauƙi

Gwamna Yahaya ya yaba da jajircewar gwamnatin APC karkashin jagorancin Tinubu, inda ya bayyana cewa shugabancinsa ya mayar da hankali kan inganta rayuwar ‘yan Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Ya jaddada cewa hangen nesan Gwamnatin Jihar Gombe ya yi daidai da manufar Shugaba Tinubu da kuma manufofin APC, wanda yace suna karfafa Shirin Sabunta Fatan.

“A matsayinmu na Shugabanni a Kungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa, yawancinmu gwamnonin APC ne, kamar yadda Gwamnatin Tarayya ita ma ta APC ce. Duk mun yi nasara ne a karkashin manufar sabunta fata, wacce ta kunshi manufofi da ka’idoji da aka gina jam’iyyarmu a kai,” in ji Gwamnan.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ceto Sauran Mutane 4 Da Aka Sace Tare Da Marigayi Janar Rabe A Katsina

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Ya ce shirin wani dandamali ne da gwamnatin APC ke amfani da shi wajen aiwatar da manufofi da tsare-tsarenta zuwa fa’idoji na zahiri ga jama’a.

Ya kara da cewa kafa kwamitoci daban-daban da aka yi ya karfafa kudurin jam’iyyar na tabbatar da dorewar shugabanci a dukkan matakai.

Da yake tsokaci kan yanayin siyasar kasar nan, Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana kwarin gwiwa game da karuwar karbuwar da jam’iyyar APC ke samu a fadin kasar nan.

Gwamnan ya yi kira ga ‘yan jam’iyyar da masu ruwa da tsaki su ci gaba da mai da hankali, su fuskanci kalubalen dake tasowa cikin himma da kuma tabbatar da cewa Shirin Sabunta Fatan ya isa kowane lungu na kasar nan.

Da yake jawabi tun farko, Malam Isa Yuguda ya ce Shirin na Sabunta Fata, Yuguda ya bayyana shi a matsayin cikakken shiri dake nufin cika alkawuran Shugaba Tinubu na inganta rayuwar talakawan Nijeriya.

Ya amince da sukar da gwamnatin ke fuskanta amma ya ce ‘yan asa da yawa ba su san kalubalen da gwamnatin ta gada ba, ciki har da cire tallafin mai, da raguwar asusun ajiyar kasashen waje da kuma karuwar basussukan cikin gida.

A cewar Yuguda, yanzu shirin zai mayar da hankali kan wayar da kan ‘yan Nijeriya game da manufofin gwamnati, da sauye-sauye da shirye-shiryen ci gaba, yayin da zai kasance dandamalin damawa da jama’a da tallafa musu.

“Wannan shiri ba na raba shinkafa ko gari bane. Ya hada da horar da jama’a kan kananan kasuwanci da sana’o’i da tabbatar da cewa ana sayan kayayyakinsu don kar su yi asara. Manufarmu ita ce tallafawa kimanin mutane 1,000 a kowace gunduma a duk fadin kasar nan. Ko da kaso 50 cikin dari aka cimma to an samu babbar nasara,” in ji shi.

Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Sojoji Sun Ceto Sauran Mutane 4 Da Aka Sace Tare Da Marigayi Janar Rabe A Katsina
Labarai

Sojoji Sun Ceto Sauran Mutane 4 Da Aka Sace Tare Da Marigayi Janar Rabe A Katsina

June 17, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Labarai

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

June 17, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Manyan Labarai

Mata Ta Hallaka Mijinta Da Wuƙa Watanni Biyu Bayan Aure A Kano

June 17, 2026
Next Post
Malami Zai San Makomar Neman Belinsa  Ranar 7 ga Janairu

Malami Zai San Makomar Neman Belinsa  Ranar 7 ga Janairu

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ceto Sauran Mutane 4 Da Aka Sace Tare Da Marigayi Janar Rabe A Katsina

Sojoji Sun Ceto Sauran Mutane 4 Da Aka Sace Tare Da Marigayi Janar Rabe A Katsina

June 17, 2026
Lionel Messi: Mutum Ko Aljan

Lionel Messi: Mutum Ko Aljan

June 17, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

June 17, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Mata Ta Hallaka Mijinta Da Wuƙa Watanni Biyu Bayan Aure A Kano

June 17, 2026
An Kaddamar Da Wani Kwas Na Horar Da Kwararru Kan Killace Kananan Makamai Na Sin Da MDD Da Afirka 

An Kaddamar Da Wani Kwas Na Horar Da Kwararru Kan Killace Kananan Makamai Na Sin Da MDD Da Afirka

June 17, 2026
An Kaddamar Da Wani Kwas Na Horar Da Kwararru Kan Killace Kananan Makamai Na Sin Da MDD Da Afirka 

An Kaddamar Da Wani Kwas Na Horar Da Kwararru Kan Killace Kananan Makamai Na Sin Da MDD Da Afirka 

June 17, 2026
Mataimakin Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Shugabanni Game Da Barkewar Cutar Ebola

Mataimakin Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Shugabanni Game Da Barkewar Cutar Ebola

June 16, 2026
Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Dakatar Da INEC Game Da Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu

Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Dakatar Da INEC Game Da Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu

June 16, 2026
Tattalin Arzikin Sin Ya Tafiya Cikin Kwanciyar Hankali

Tattalin Arzikin Sin Ya Tafiya Cikin Kwanciyar Hankali

June 16, 2026
Gaza

Farashin Mai Ya Faɗi Ƙasa Da Dala 80 Bayan cimma Yarjejeniyar Amurka Da Iran

June 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.