ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sabon Shirin Sabunta Fata Shi Ne Ƙashin Bayan Ci Gaban Kasa – Gwamna Gombe

by Leadership Hausa
8 months ago
gombe

Khalid Idris Doya

Gwamnan Jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya, ya bayyana shirin Sabunta Fata na Shugaba Bola Ahmed Tinubu a matsayin salon gwamnatocin da APC ke jagoranta a dukkan matakai don aiwatar da ayyukansu ga ‘yan Nijeriya.

Gwamnan ya yi wannan jawabin ne yayin da ya karbi bakuncin Ko-odinetan Shirin Sabunta Fata na Yankin Arewa Maso Gabas kuma tsohon Gwamnan Jihar Bauchi, Malam Isa Yuguda, a fadar Gwamnati da ke Gombe.

  • Buƙatar A Sake Duba Sabuwar Dokar Haraji
  • Shari’ar Annabi SAW Ta Fi Ta Sauran Annabawa Sauƙi

Gwamna Yahaya ya yaba da jajircewar gwamnatin APC karkashin jagorancin Tinubu, inda ya bayyana cewa shugabancinsa ya mayar da hankali kan inganta rayuwar ‘yan Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Ya jaddada cewa hangen nesan Gwamnatin Jihar Gombe ya yi daidai da manufar Shugaba Tinubu da kuma manufofin APC, wanda yace suna karfafa Shirin Sabunta Fatan.

“A matsayinmu na Shugabanni a Kungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa, yawancinmu gwamnonin APC ne, kamar yadda Gwamnatin Tarayya ita ma ta APC ce. Duk mun yi nasara ne a karkashin manufar sabunta fata, wacce ta kunshi manufofi da ka’idoji da aka gina jam’iyyarmu a kai,” in ji Gwamnan.

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ya ce shirin wani dandamali ne da gwamnatin APC ke amfani da shi wajen aiwatar da manufofi da tsare-tsarenta zuwa fa’idoji na zahiri ga jama’a.

Ya kara da cewa kafa kwamitoci daban-daban da aka yi ya karfafa kudurin jam’iyyar na tabbatar da dorewar shugabanci a dukkan matakai.

Da yake tsokaci kan yanayin siyasar kasar nan, Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana kwarin gwiwa game da karuwar karbuwar da jam’iyyar APC ke samu a fadin kasar nan.

Gwamnan ya yi kira ga ‘yan jam’iyyar da masu ruwa da tsaki su ci gaba da mai da hankali, su fuskanci kalubalen dake tasowa cikin himma da kuma tabbatar da cewa Shirin Sabunta Fatan ya isa kowane lungu na kasar nan.

Da yake jawabi tun farko, Malam Isa Yuguda ya ce Shirin na Sabunta Fata, Yuguda ya bayyana shi a matsayin cikakken shiri dake nufin cika alkawuran Shugaba Tinubu na inganta rayuwar talakawan Nijeriya.

Ya amince da sukar da gwamnatin ke fuskanta amma ya ce ‘yan asa da yawa ba su san kalubalen da gwamnatin ta gada ba, ciki har da cire tallafin mai, da raguwar asusun ajiyar kasashen waje da kuma karuwar basussukan cikin gida.

A cewar Yuguda, yanzu shirin zai mayar da hankali kan wayar da kan ‘yan Nijeriya game da manufofin gwamnati, da sauye-sauye da shirye-shiryen ci gaba, yayin da zai kasance dandamalin damawa da jama’a da tallafa musu.

“Wannan shiri ba na raba shinkafa ko gari bane. Ya hada da horar da jama’a kan kananan kasuwanci da sana’o’i da tabbatar da cewa ana sayan kayayyakinsu don kar su yi asara. Manufarmu ita ce tallafawa kimanin mutane 1,000 a kowace gunduma a duk fadin kasar nan. Ko da kaso 50 cikin dari aka cimma to an samu babbar nasara,” in ji shi.

Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja
  • Leadership Hausa
    Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed
  • Leadership Hausa
    Batun Dawo Da Tallafin Mai Da Atiku Ya Yi Na Ci Gaba Da Tayar Da Kura
  • Leadership Hausa
    Batun Guguwar Kakar Yakin Neman Zabukan 2027 A Nijeriya

MASU ALAKA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Next Post
Malami Zai San Makomar Neman Belinsa  Ranar 7 ga Janairu

Malami Zai San Makomar Neman Belinsa  Ranar 7 ga Janairu

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.