ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sabon Shirin Sabunta Fata Shi Ne Ƙashin Bayan Ci Gaban Kasa – Gwamna Gombe

by Leadership Hausa
6 months ago
gombe

Khalid Idris Doya

Gwamnan Jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya, ya bayyana shirin Sabunta Fata na Shugaba Bola Ahmed Tinubu a matsayin salon gwamnatocin da APC ke jagoranta a dukkan matakai don aiwatar da ayyukansu ga ‘yan Nijeriya.

Gwamnan ya yi wannan jawabin ne yayin da ya karbi bakuncin Ko-odinetan Shirin Sabunta Fata na Yankin Arewa Maso Gabas kuma tsohon Gwamnan Jihar Bauchi, Malam Isa Yuguda, a fadar Gwamnati da ke Gombe.

  • Buƙatar A Sake Duba Sabuwar Dokar Haraji
  • Shari’ar Annabi SAW Ta Fi Ta Sauran Annabawa Sauƙi

Gwamna Yahaya ya yaba da jajircewar gwamnatin APC karkashin jagorancin Tinubu, inda ya bayyana cewa shugabancinsa ya mayar da hankali kan inganta rayuwar ‘yan Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Ya jaddada cewa hangen nesan Gwamnatin Jihar Gombe ya yi daidai da manufar Shugaba Tinubu da kuma manufofin APC, wanda yace suna karfafa Shirin Sabunta Fatan.

“A matsayinmu na Shugabanni a Kungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa, yawancinmu gwamnonin APC ne, kamar yadda Gwamnatin Tarayya ita ma ta APC ce. Duk mun yi nasara ne a karkashin manufar sabunta fata, wacce ta kunshi manufofi da ka’idoji da aka gina jam’iyyarmu a kai,” in ji Gwamnan.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

Ya ce shirin wani dandamali ne da gwamnatin APC ke amfani da shi wajen aiwatar da manufofi da tsare-tsarenta zuwa fa’idoji na zahiri ga jama’a.

Ya kara da cewa kafa kwamitoci daban-daban da aka yi ya karfafa kudurin jam’iyyar na tabbatar da dorewar shugabanci a dukkan matakai.

Da yake tsokaci kan yanayin siyasar kasar nan, Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana kwarin gwiwa game da karuwar karbuwar da jam’iyyar APC ke samu a fadin kasar nan.

Gwamnan ya yi kira ga ‘yan jam’iyyar da masu ruwa da tsaki su ci gaba da mai da hankali, su fuskanci kalubalen dake tasowa cikin himma da kuma tabbatar da cewa Shirin Sabunta Fatan ya isa kowane lungu na kasar nan.

Da yake jawabi tun farko, Malam Isa Yuguda ya ce Shirin na Sabunta Fata, Yuguda ya bayyana shi a matsayin cikakken shiri dake nufin cika alkawuran Shugaba Tinubu na inganta rayuwar talakawan Nijeriya.

Ya amince da sukar da gwamnatin ke fuskanta amma ya ce ‘yan asa da yawa ba su san kalubalen da gwamnatin ta gada ba, ciki har da cire tallafin mai, da raguwar asusun ajiyar kasashen waje da kuma karuwar basussukan cikin gida.

A cewar Yuguda, yanzu shirin zai mayar da hankali kan wayar da kan ‘yan Nijeriya game da manufofin gwamnati, da sauye-sauye da shirye-shiryen ci gaba, yayin da zai kasance dandamalin damawa da jama’a da tallafa musu.

“Wannan shiri ba na raba shinkafa ko gari bane. Ya hada da horar da jama’a kan kananan kasuwanci da sana’o’i da tabbatar da cewa ana sayan kayayyakinsu don kar su yi asara. Manufarmu ita ce tallafawa kimanin mutane 1,000 a kowace gunduma a duk fadin kasar nan. Ko da kaso 50 cikin dari aka cimma to an samu babbar nasara,” in ji shi.

Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

MASU ALAKA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Next Post
Malami Zai San Makomar Neman Belinsa  Ranar 7 ga Janairu

Malami Zai San Makomar Neman Belinsa  Ranar 7 ga Janairu

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.