ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sarki Sanusi Ya Goyi Bayan Karfafa Tattalin Arzikin Mata

by Sani Anwar
3 months ago
Mata

Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, ya ce; ya kamata a yi watsi da labaran da ke nuna yadda mata ke shiga harkokin tattalin arziki a matsayin wani ra’ayi na kasashen waje, yana mai jaddada cewa; Musulunci ya bai wa mata ‘yancin cin gashin kai.

Sanusi ya bayyana haka ne, a lokacin kaddamar da manufar karfafa tattalin arzikin mata (WEE) a hukumance ga Jihar Kano, wanda aka bunkasa ta hanyar hadin gwiwa da Cibiyar Bincike da Ayyuka (dRPC), tare da tallafin abokan hadin gwiwa da suka hada da Ford Foundation, Asusun Kalubalantar Kasuwancin Afirka da Gidauniyar Gates.

  • Kawar Da Dukkanin Haraji Kan Hajojin Da Ake Shigarwa Kasar Sin Daga Afirka Zai Bunkasa Cinikayyar Albarkatun Gona Na Afirka Ta Kudu
  • Kudaden Shiga Na Masana’Antun Kimiya Da Fasaha Na Kasar Sin Ya Karu Da 16.1% a Watannin Janairu Da Fabrairun Wannan Shekara

Sarkin ya ce, ci gaban al’ummar Musulmi na farko, ya ginu ne a kan yadda mata za su shiga harkar kasuwanci da bayar da tallafin karatu da kuma jagorancin al’umma, inda ya ce; karfafa wa tattalin arzikin mata, ya yi daidai da koyarwar Musulunci da kuma tarihin Kano.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, Kano ba za ta iya samun ci gaba mai dorewa ba, idan har mata suka ci gaba da zama saniyar ware.

“Tarihinmu da imaninmu a bayyane yake, domin kuwa, Musulunci ya bai wa mata ‘yancin mallakar kadarori, gado, kasuwanci da kuma harkokin tattalin arziki mai zaman kansa. Dole ne mu yi watsi da duk wani labari da ke nuna karfafa tattalin arzikin mata a matsayin bako ga kimarmu,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Sanusi ya kara da cewa, idan har Kano za ta yi gogayya a fannin tattalin arzikin duniya, dole ne ta yi amfani da basirar mata da kuma samar da ayyukan yi, tare da tabbatar da cewa; ‘ya’ya mata sun samu ilimi da fasahar zamani da ake bukata a tattalin arzikin zamani.

Har ila yau, sarkin ya yi alkawarin tallafa wa Majalisar Masarautar Kano, wajen inganta manufofin, gami da bayar da shawarwari kan ilimin ’ya’ya mata, kula da zamantakewar al’umma da kuma karbuwar da al’umma ke yi na sana’ar mata.

Da yake yin jawabi a wajen taron, Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, wanda kwamishinan raya karkara da al’adu, Abdulkadir Abdulsalam ya wakilta, ya bayyana kaddamar da manufofin a matsayin wani ci gaba a yunkurin jihar, na samar da ci gaba.

Ya ce, gwamnati ta fara aiwatar da matakan tallafa wa mata ta hanyar kason kasafin kudi da kuma bayar da tallafin naira 50,000 ga mata 5,200 a duk wata a fadin kananan hukumomi 484 na jihar.

Ita ma wadda ta kafa kungiyar Isa Wali Empowerment Initiatibe, Maryam Uwais, ta bukaci masu ruwa da tsaki, da su tabbatar ba a bar matan karkara da ‘yan mata a baya ba.

Manufar shirin na nufin fitar da mata kimanin miliyan biyu daga kangin talauci tare da ba da gudummawar kusan kashi 30 cikin 100 na ci gaban tattalin arzikin Kano.

Mata
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

MASU ALAKA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
Next Post
2023: Me Ya Sa Ake Rububin Wike?

Wike Ya Bukaci Bangarorin PDP Su Hada Kai Kafin Zaben 2027

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.