ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sarki Sanusi Ya Goyi Bayan Karfafa Tattalin Arzikin Mata

by Sani Anwar
3 months ago
Mata

Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, ya ce; ya kamata a yi watsi da labaran da ke nuna yadda mata ke shiga harkokin tattalin arziki a matsayin wani ra’ayi na kasashen waje, yana mai jaddada cewa; Musulunci ya bai wa mata ‘yancin cin gashin kai.

Sanusi ya bayyana haka ne, a lokacin kaddamar da manufar karfafa tattalin arzikin mata (WEE) a hukumance ga Jihar Kano, wanda aka bunkasa ta hanyar hadin gwiwa da Cibiyar Bincike da Ayyuka (dRPC), tare da tallafin abokan hadin gwiwa da suka hada da Ford Foundation, Asusun Kalubalantar Kasuwancin Afirka da Gidauniyar Gates.

  • Kawar Da Dukkanin Haraji Kan Hajojin Da Ake Shigarwa Kasar Sin Daga Afirka Zai Bunkasa Cinikayyar Albarkatun Gona Na Afirka Ta Kudu
  • Kudaden Shiga Na Masana’Antun Kimiya Da Fasaha Na Kasar Sin Ya Karu Da 16.1% a Watannin Janairu Da Fabrairun Wannan Shekara

Sarkin ya ce, ci gaban al’ummar Musulmi na farko, ya ginu ne a kan yadda mata za su shiga harkar kasuwanci da bayar da tallafin karatu da kuma jagorancin al’umma, inda ya ce; karfafa wa tattalin arzikin mata, ya yi daidai da koyarwar Musulunci da kuma tarihin Kano.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, Kano ba za ta iya samun ci gaba mai dorewa ba, idan har mata suka ci gaba da zama saniyar ware.

“Tarihinmu da imaninmu a bayyane yake, domin kuwa, Musulunci ya bai wa mata ‘yancin mallakar kadarori, gado, kasuwanci da kuma harkokin tattalin arziki mai zaman kansa. Dole ne mu yi watsi da duk wani labari da ke nuna karfafa tattalin arzikin mata a matsayin bako ga kimarmu,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Sanusi ya kara da cewa, idan har Kano za ta yi gogayya a fannin tattalin arzikin duniya, dole ne ta yi amfani da basirar mata da kuma samar da ayyukan yi, tare da tabbatar da cewa; ‘ya’ya mata sun samu ilimi da fasahar zamani da ake bukata a tattalin arzikin zamani.

Har ila yau, sarkin ya yi alkawarin tallafa wa Majalisar Masarautar Kano, wajen inganta manufofin, gami da bayar da shawarwari kan ilimin ’ya’ya mata, kula da zamantakewar al’umma da kuma karbuwar da al’umma ke yi na sana’ar mata.

Da yake yin jawabi a wajen taron, Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, wanda kwamishinan raya karkara da al’adu, Abdulkadir Abdulsalam ya wakilta, ya bayyana kaddamar da manufofin a matsayin wani ci gaba a yunkurin jihar, na samar da ci gaba.

Ya ce, gwamnati ta fara aiwatar da matakan tallafa wa mata ta hanyar kason kasafin kudi da kuma bayar da tallafin naira 50,000 ga mata 5,200 a duk wata a fadin kananan hukumomi 484 na jihar.

Ita ma wadda ta kafa kungiyar Isa Wali Empowerment Initiatibe, Maryam Uwais, ta bukaci masu ruwa da tsaki, da su tabbatar ba a bar matan karkara da ‘yan mata a baya ba.

Manufar shirin na nufin fitar da mata kimanin miliyan biyu daga kangin talauci tare da ba da gudummawar kusan kashi 30 cikin 100 na ci gaban tattalin arzikin Kano.

Mata
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Sojoji Sun Ceto Mutum 92 Tare Da Daƙile Harin Ƴan Ta’adda A Borno
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Uzodimma: Babu Dimokraɗiyya Idan Babu Hamayya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Alamomin Fara Ruɓewar Hannu Bayan Ɗorin Gida
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ministocin Da Suka Ajiye Muƙamansu Ba Su Samu Tikitin Takara Ba

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
2023: Me Ya Sa Ake Rububin Wike?

Wike Ya Bukaci Bangarorin PDP Su Hada Kai Kafin Zaben 2027

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.