ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sarki Sanusi Ya Goyi Bayan Karfafa Tattalin Arzikin Mata

by Sani Anwar
6 months ago
Mata

Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, ya ce; ya kamata a yi watsi da labaran da ke nuna yadda mata ke shiga harkokin tattalin arziki a matsayin wani ra’ayi na kasashen waje, yana mai jaddada cewa; Musulunci ya bai wa mata ‘yancin cin gashin kai.

Sanusi ya bayyana haka ne, a lokacin kaddamar da manufar karfafa tattalin arzikin mata (WEE) a hukumance ga Jihar Kano, wanda aka bunkasa ta hanyar hadin gwiwa da Cibiyar Bincike da Ayyuka (dRPC), tare da tallafin abokan hadin gwiwa da suka hada da Ford Foundation, Asusun Kalubalantar Kasuwancin Afirka da Gidauniyar Gates.

  • Kawar Da Dukkanin Haraji Kan Hajojin Da Ake Shigarwa Kasar Sin Daga Afirka Zai Bunkasa Cinikayyar Albarkatun Gona Na Afirka Ta Kudu
  • Kudaden Shiga Na Masana’Antun Kimiya Da Fasaha Na Kasar Sin Ya Karu Da 16.1% a Watannin Janairu Da Fabrairun Wannan Shekara

Sarkin ya ce, ci gaban al’ummar Musulmi na farko, ya ginu ne a kan yadda mata za su shiga harkar kasuwanci da bayar da tallafin karatu da kuma jagorancin al’umma, inda ya ce; karfafa wa tattalin arzikin mata, ya yi daidai da koyarwar Musulunci da kuma tarihin Kano.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, Kano ba za ta iya samun ci gaba mai dorewa ba, idan har mata suka ci gaba da zama saniyar ware.

“Tarihinmu da imaninmu a bayyane yake, domin kuwa, Musulunci ya bai wa mata ‘yancin mallakar kadarori, gado, kasuwanci da kuma harkokin tattalin arziki mai zaman kansa. Dole ne mu yi watsi da duk wani labari da ke nuna karfafa tattalin arzikin mata a matsayin bako ga kimarmu,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Sanusi ya kara da cewa, idan har Kano za ta yi gogayya a fannin tattalin arzikin duniya, dole ne ta yi amfani da basirar mata da kuma samar da ayyukan yi, tare da tabbatar da cewa; ‘ya’ya mata sun samu ilimi da fasahar zamani da ake bukata a tattalin arzikin zamani.

Har ila yau, sarkin ya yi alkawarin tallafa wa Majalisar Masarautar Kano, wajen inganta manufofin, gami da bayar da shawarwari kan ilimin ’ya’ya mata, kula da zamantakewar al’umma da kuma karbuwar da al’umma ke yi na sana’ar mata.

Da yake yin jawabi a wajen taron, Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, wanda kwamishinan raya karkara da al’adu, Abdulkadir Abdulsalam ya wakilta, ya bayyana kaddamar da manufofin a matsayin wani ci gaba a yunkurin jihar, na samar da ci gaba.

Ya ce, gwamnati ta fara aiwatar da matakan tallafa wa mata ta hanyar kason kasafin kudi da kuma bayar da tallafin naira 50,000 ga mata 5,200 a duk wata a fadin kananan hukumomi 484 na jihar.

Ita ma wadda ta kafa kungiyar Isa Wali Empowerment Initiatibe, Maryam Uwais, ta bukaci masu ruwa da tsaki, da su tabbatar ba a bar matan karkara da ‘yan mata a baya ba.

Manufar shirin na nufin fitar da mata kimanin miliyan biyu daga kangin talauci tare da ba da gudummawar kusan kashi 30 cikin 100 na ci gaban tattalin arzikin Kano.

Mata
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ko Kun San Amfanin Kwanciya Da Bangaren Hagu?
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    2027:Mata Shida Da Ke Takarar Neman Shugabancin Nijeriya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Dambarwa A Kasuwancin Iyalan Indimi
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Illar Shan Taba Sigari Da Dangoginta

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
2023: Me Ya Sa Ake Rububin Wike?

Wike Ya Bukaci Bangarorin PDP Su Hada Kai Kafin Zaben 2027

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.