Mai Alfarma Sarkin Musulmi kuma shugaban Majalisar Ƙoli ta addinn Musulunci, Muhammad Sa’ad Abubakar III, ya ayyana ranar Litinin 18 ga Mayu, 2026 a matsayin ranar farko ga watan Zul-Hijjah na shekarar 1447 bayan hijira, bayan tabbatar da ganin jinjirin watan.
Sanarwar ta fito ne cikin wata takarda da Sambo Wali Junaidu, wanda kuma shi ne shugaban kwamitin harkokin addini na masarautar Sokoto Sultanate Council, ya sanya wa hannu.
Majalisar ta bayyana cewa watan Zul-Hijjah na daga cikin watanni mafi alfarma a Musulunci, kuma shi ne watan da ake gudanar da aikin Hajji tare da bikin Eid al-Adha. Ta kuma ce ana sa ran bikin Eid-El-Kabir zai kasance ranar Laraba 27 ga Mayu, 2026 wanda zai yi daidai da 10 ga Zul-Hijjah.
Sarkin Musulmin ya buƙaci al’ummar Musulmi su yi amfani da wannan lokaci wajen ƙara yawan ibada, da addu’o’i da neman zaman lafiya da haɗin kai a Nijeriya. Haka kuma ya gargaɗi jama’a da su riƙa dogaro da sahihan bayanai daga majalisar masarautar da hukumomin addini da aka amince da su kawai.














Discussion about this post