Aƙalla ’yan majalisar tarayya takwas ne suka rasa tikitin komawa majalisar tarayya a zaɓen fidda gwani na jam’iyyar APC a jihar Katsina gabanin zaɓen 2027. Jihar na da kujerun majalisar wakilai guda 15 kuma gaba ɗayansu suna hannun APC.
Daga cikin waɗanda suka rasa tikitin akwai Sani Aliyu Danlami mai wakiltar Katsina ta Tsakiya, Aminu Jamoh mai wakiltar Daura/Sandamu/Mai’adua, da Sani Lawal mai wakiltar Ɓaure/Zango. Sauran sun haɗa da Abubakar Yahaya, Ahmad Yusuf Ibrahim da Ahmad Abubakar.
Haka kuma Dalhatu Tafoki mai wakiltar Kankara/Sabuwa/Faskari, wanda ya sauya sheka zuwa PDP, ya samu tikitin komawa majalisar a sabuwar jam’iyyarsa. Kazalika, Sanata mai wakiltar Daura, Nasiru Sani Zango, shi ma ya rasa tikitin komawa majalisar dattawa.
A gefe guda kuma, wasu ’yan majalisa uku da suka sauya sheka daga PDP zuwa APC sun samu tikitin takara kai tsaye. Sun haɗa da Salisu Yusuf Majigiri, da Aliyu Iliyasu da A.B Dabai, waɗanda dukkansu suka samu tikitin tsayawa takara a ƙarƙashin APC domin zaɓen 2027.















Discussion about this post